• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Xi Ta APEC Na Nuni Da Kyakkyawar Sakamakon Yunkurin Daidata Dangantakar Sin Da Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ziyarar Xi Ta APEC Na Nuni Da Kyakkyawar Sakamakon Yunkurin Daidata Dangantakar Sin Da Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa gayyatar da shugaban kasar Amurka Joe Biden ya yi masa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarci taron kolin kasashen Sin da Amurka, da taron shugabannin tattalin arzikin Asiya da Fasifik (APEC) karo na 30 da aka shirya gudanarwa a wannan mako a San Francisco. Kafin a kai ga wannan mataki mai nuni da murmurewar dangantakar kasashen biyu da ta yi tsami a cikin ’yan shekarun nan har ma ta kai ga “yakin mummuke”, bari mu waiwayi kadan daga cikin mu’amalolin baya-bayan nan da suka wakana tsakanin kasashen biyu kawo yanzu. 

Tun daga watan Yunin bana ne manyan jami’an Amurka da suka hada da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken, da sakatariyar baitulmali Janet Yellen da sakatariyar kasuwanci Gina Raimondo suka ziyarci kasar Sin bi da bi. Bugu da kari, tattaunawar da aka yi tsakanin wakilin musamman na kasar Sin kan sauyin yanayi Xie Zhenhua da takwaransa na Amurka John Kerry a jihar California ta samu sakamako mai kyau. Daga bisani kasashen biyu sun kafa kungiyoyin harkar tattalin arziki da na kudi da sauran hanyoyin musaya da hada-hadar kudi da cinikayya.

  • Firaministan Pakistan Kakar: Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Tana Girmama Bambance-bambance A Tsakanin Kasa Da Kasa
  • Yawan Kayayyaki Da Aka Yi Jigilarsu Na Kasar Sin Ya Kai Matsayi Mafi Girma A Bikin Sayayya Ta “Double 11” 

A karshen watan Oktoba kuma, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya kai ziyara kasar Amurka, inda ya gana da Biden, ya kuma tattauna da wasu manyan jami’an siyasa, da masu ruwa da tsaki da ’yan kasuwa na Amurka. Kazalika, He Lifeng, mataimakin firaministan gwamnatin kasar Sin, kana shugaban kwamitin harkokin tattalin arziki da kasuwancin Sin da Amurka na kasar Sin, shi ma ya ziyarci Amurka daga ranar 8 zuwa 12 ga wannan watan Nuwamba.

A karon farko, Amurka ta aika da wata babbar tawaga zuwa bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin karo na shida (CIIE) da aka kammala a Juma’ar makon jiya. Ana ci gaba da yin mu’amala mai zurfi, kuma dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta nuna alamun murmurewa.

Ginshikin alakar Sin da Amurka na dogaro ne da mu’amala tsakanin al’umman kasashen biyu. Kama daga ’yan kasuwan Amurka dake ziyara a kasar Sin, zuwa shirin “Bond with Guling: dandalin sada zumunta tsakanin Sin da Amurka na shekarar 2023,” da kuma tawagar wakilan Flying Tigers na Amurka da suka ziyarci kasar Sin, duka wadannan mu’amaloli sun nuna kyakkyawar fahimta da zurfafa zumunci, wanda hakan ya kara karfafa zumunci da hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Ana sa ran halartar shugaba Xi a taron kolin Sin da Amurka da taron kolin kungiyar APEC zai tabbatar da fahimtar ci gaban kasar Sin dake dauke da tarihi mai muhimmanci, da taimakawa kasashen duniya samun karin wadanda za su jagoranci ci gaban duniya ta hanyar yin amfani da tsarin zamanantarwa irin ta kasar Sin.

A gun taron kungiyar APEC da za a yi, kasar Sin za ta ci gaba da daukar nauyin da ya rataya a wuyanta a matsayinta na babbar kasa, da kokarin tabbatar da cewa kasuwanni masu tasowa da kasashe masu tasowa sun fi samun wakilci, da damar bayyana ra’ayoyinsu a harkokin duniya, da kuma sa kaimi ga ci gaba da kyautata tsarin mulkin duniya. (Muhammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaBidenXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-yanzu: Saudiyya Ta Soke Bizar ‘Yan Nijeriya 264 Bayan Sun Isa Jeddah

Next Post

Ganawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Za Su Yi Za Ta Iya Amfanin Duniya

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

5 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

6 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

7 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

8 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

9 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

19 hours ago
Next Post
Ganawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Za Su Yi Za Ta Iya Amfanin Duniya

Ganawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Za Su Yi Za Ta Iya Amfanin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.