• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zulum Ya Shigar Da Marayu 7000 Makaranta A Monguno

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Zulum Ya Shigar Da Marayu 7000 Makaranta A Monguno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ci gaba da kokarin sake farfado da harkokin ilimi tare da karfafa gwiwar jama’a wajen sake tsugunnar da ‘yan gudun hijira a yankunan da rikicin Boko Haram ya tagayyra tare da samar da zaman lafiya ga al’umma, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya ziyarci Kasuwar Cross-Kauwa wadda a da sansanin ce ga mayakan Boko Haram a karamar hukumar Kukawa a arewacin Jihar Borno.

Gwamna Zulum ya shigar da ‘ya’yan ‘yan gudun hijira da marayun da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu kimanin 7000 zuwa makarantun Boko a garin Monguno.

  • Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wani Masallaci Ya Kashe Akalla Mutane 18 A Afganistan
  • A KUSKURA: Yadda Kayan Maye Ya Zama Ruwan Dare A Tsakanin Al’umma

Ya ce gwamnatinsa tana da kyakkyawan shirin fadada shigar da yara makarantun, wanda rajistar zai tashi daga 7000 zuwa 10,000 nan gaba.

Gwamnan ya tabbatar wa da al’ummar yankin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da bai wa jami’an tsaro dukkan goyon bayan da ya dace domin ganin an samu zaman lafiya a yankunan tare da shan alwashin sake bude kasuwanni idan abubuwa suka kyautata.

 Har ila yau, Gwamna Zulum ya jaddada cewa samar da abin dogaro da kai ga jama’a shi ne babban makami mai inganci wajen dakile duk wani yunkurin masu tayar da kayar baya.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Ya ce zama a sansanonin ‘yan gudun hijira ba shi da wata ma’ana, don haka a tallafa wa mutane domin su samu abin dogaro da kai shi ne ya fi dacewa.

Gwamnan ya yaba wa kokarin gwamnatin tarayya a karkashin Shugaban kasa Muhammdu Buhari da kuma rundunar sojojin Nijeriya da sauran masu ruwa da tsaki wadanda suka bayar da gudunmawa wajen samar da zaman lafiya a Jihar Borno.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramBornoZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Rugujewar Gadar Katarko Ta Katse Yobe Da Jihohin Borno Da Gombe

Next Post

Dan Takarar Gwamnan Jihar Ogun Na PRP Bamgbose Ya Mutu , Yana Da Shekara 54

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

3 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

6 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

6 hours ago
Zulum
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

8 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

9 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

10 hours ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan Jihar Ogun Na PRP Bamgbose Ya Mutu , Yana Da Shekara 54

Dan Takarar Gwamnan Jihar Ogun Na PRP Bamgbose Ya Mutu , Yana Da Shekara 54

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Zulum

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.