• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makarantar ‘Family Support Programme’ Ta Shirya Taron Lakcoci Ga Ɗalibai Sama Da 100 A Katsina

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makarantar ‘Family Support Programme’  Ta Shirya Taron Lakcoci Ga Ɗalibai Sama Da 100 A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar tsofaffin ɗaliban makarantar Family Support Programme wato Family Support Programme Old Students Association (FASPOSA) ajin 2018 ta shirya taron lakcoci daban-daban ga ɗalibai sama da guda 100 ‘yan makarantar.

Taron ya gudana ne a babban ɗakin taron makarantar kuma ya samu halartar wasu daga cikin malamai, mambobi da shugabannin ƙungiyar, har ma da manyan baƙin da suka zo daga wajen makarantar.

  • Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara
  • “CBN Na Da Goyon Bayana Wajen Sauya Fasalin Naira” —Buhari

Taken taron mai suna ‘CHANGE THE WORLD’ wato ‘A CANZA DUNIYA’ ya samo asali ne bisa irin yadda matasa masu tasowa suke da muhimmiyar rawa wurin canza duniya.

Tsofaffin
Wasu daga cikin shugabannin kungiyar tsofaffin daliban makarantar mata

Batutuwan da aka yi lakca akan su sun haɗa da; muhimmancin sana’a a ƙarni na ashirin da ɗaya, illar shaye-shaye da kuma rashin maida hankalin ɗalibai a makarantun Sakandare.

Daga bisani kuma, an gabatar da wasannin kwaikwayo tare da rubutattun waƙoƙin harshen Turanci masu nishaɗantarwa, wa’azantarwa, ilimantarwa da ƙayatarwa.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Tsofaffin
Wasu daga cikin shugabannin kungiyar tsofaffin daliban makarantar mata

Da yake jawabi a lokacin taron, shugaban ƙungiyar Auwal Ibrahim, ya bayyana cewa an shirya wannan taron wayar da kai ga daliban domin ilimantar da su akan illar shan miyagun ƙwayoyi, illar satar jarabawa da yadda za su koyi sana’o’i domin dogaro da kansu.

Ya yi kira ga dukkan daliban da su ƙaurace tare da nisantar dukkanin wani nau’in kayan maye saboda hakan ka iya sa rayuwarsu cikin halin ƙaƙani’kayi da lalacewar rayuwa, saboda hakan domin ganin sun inganta rayuwa to tabbas su tabbatar sun guji tare da nisantar kayan maye.

Domin ta’ammali da miyagun ƙwayoyi babu abin da yake jaza wa sai lalata rayuwa.

Tsofaffin
Wasu daga cikin shugabannin kungiyar tsofaffin daliban makarantar

Mataimakiyar shugaban kungiyar, Maryam Aminu Saulawa a jawabin da ta yi kira ga dalibai musamman mata akan muhimmancin ilimin ƴaƴa mata, inda ta jawo hankalinsu da su maida hankali akan karatunsu domin ganin sun cimma gaci a rayuwarsu ta nan gaba.

Ta yi kira ga ƴaƴa mata da su kuma tashi su nemi sana’a musamman ƙananan sana’o’i irin wanda mata ke iyayi a cikin gida ba tare da sun bar gidajen iyayansu ba, domin hakan zai taimaka wa rayuwar wajen ganin cewa sun dogara da kansu.

Wakilin shugabar makarantar malam Abubakar Sa’idu, ta nuna jin daɗinta bisa yadda daliban suka cimma nasara a rayuwarsu, da ya sanya suka waiwayo ƙannensu domin bada gudunmawarsu ga ci gaban makarantar.

Tsofaffin
Dalibai na sauraren lakca

Abubakar Sa’idu, ya ce makarantar tana alfahari da su kan wannan kyakkyawan aiki da suke yi, sai ya buƙace su da su ɗore da hakan domin cibgaban ilimi a makarantar da Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya, da kuma samar da al’umma tsaftatacciya.

A jawabinsu daban-daban uwar ƙungiyar Misis Fatima Abdullahi da Misis Hajara Korau da kuma malam Musa Umar sun jinjina wa tsofaffin daliban a bisa shirya wannan taro, inda suka bayyana cewa abubuwan da suka tattauna ya yi dai-dai da matsalolin da ake fuskanta a Jihar Katsina, wanda ake buƙatar gudunmuwar kowa a kan haka.

A jawabin skataren ƙungiyar, Sulaiman Nasir shi ma yayi kira ga daliban maza da mata da su maida hankali a karatunsu kuma su ƙauracewa duk wata hanya da ka iya jaza musu satar amsa a lokacin jarabawa, saboda hakan babbar illa ce ga ɗalibi mai neman ilimi.

Tsofaffin
Wasu daga cikin daliban da aka shirya wa lakca

Sakataren ƙungiyar ya kuma kara da cewa su tashi su nemi sana’a musamman maza, inda ya ce za su iya fara koyon aikin hannu misali: kafinta, kanikanci, fenti, gyaran wutar lantarki da dai sauransu, tun daga yanzu, wato tun suna da ƙuruciyarsu domin hakan zai taimaka musu, da kuma inganta rayuwarsu a shekaru masu zuwa.

Abdulrahman Ibrahim Hassan, jami’in hulda da jama’a na ƙungiyar, ya ce wannan shi ne karon farko da wannan ƙungiya ta shirya irin wannan taro domin ci gaban ɗalibai, ya kuma kara da cewa “In sha Allahu za mu ci gaba da aiwatar da dukkan kyawawan abubuwa ire-iren waɗannan domin ci gaban ɗalibai da matasa har ma da sauran al’umma.”

Daga ƙarshe, malamai da hukumar makarantar sun nuna jin daɗinsu akan irin wannan ci gaba da tsofaffin ɗalibanta suka kawo, sun kuma yi godiya tare da jaddada goyon bayansu akan dukkan abubuwa irin waɗannan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci Gaban MatasaKatsinaKungiyar Tsofaffin DalibaiLakcociMakaranta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara

Next Post

Mutuwar Dan Davido: PDP Ta Dakatar Da Tarukan Siyasa A Jihar Osun

Related

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe
Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

8 hours ago
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano
Labarai

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

11 hours ago
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

12 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

15 hours ago
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

17 hours ago
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
Labarai

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

18 hours ago
Next Post
Mutuwar Dan Davido: PDP Ta Dakatar Da Tarukan Siyasa A Jihar Osun

Mutuwar Dan Davido: PDP Ta Dakatar Da Tarukan Siyasa A Jihar Osun

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

May 12, 2025
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.