• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makarantar ‘Family Support Programme’ Ta Shirya Taron Lakcoci Ga Ɗalibai Sama Da 100 A Katsina

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makarantar ‘Family Support Programme’  Ta Shirya Taron Lakcoci Ga Ɗalibai Sama Da 100 A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar tsofaffin ɗaliban makarantar Family Support Programme wato Family Support Programme Old Students Association (FASPOSA) ajin 2018 ta shirya taron lakcoci daban-daban ga ɗalibai sama da guda 100 ‘yan makarantar.

Taron ya gudana ne a babban ɗakin taron makarantar kuma ya samu halartar wasu daga cikin malamai, mambobi da shugabannin ƙungiyar, har ma da manyan baƙin da suka zo daga wajen makarantar.

  • Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara
  • “CBN Na Da Goyon Bayana Wajen Sauya Fasalin Naira” —Buhari

Taken taron mai suna ‘CHANGE THE WORLD’ wato ‘A CANZA DUNIYA’ ya samo asali ne bisa irin yadda matasa masu tasowa suke da muhimmiyar rawa wurin canza duniya.

Tsofaffin
Wasu daga cikin shugabannin kungiyar tsofaffin daliban makarantar mata

Batutuwan da aka yi lakca akan su sun haɗa da; muhimmancin sana’a a ƙarni na ashirin da ɗaya, illar shaye-shaye da kuma rashin maida hankalin ɗalibai a makarantun Sakandare.

Daga bisani kuma, an gabatar da wasannin kwaikwayo tare da rubutattun waƙoƙin harshen Turanci masu nishaɗantarwa, wa’azantarwa, ilimantarwa da ƙayatarwa.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Tsofaffin
Wasu daga cikin shugabannin kungiyar tsofaffin daliban makarantar mata

Da yake jawabi a lokacin taron, shugaban ƙungiyar Auwal Ibrahim, ya bayyana cewa an shirya wannan taron wayar da kai ga daliban domin ilimantar da su akan illar shan miyagun ƙwayoyi, illar satar jarabawa da yadda za su koyi sana’o’i domin dogaro da kansu.

Ya yi kira ga dukkan daliban da su ƙaurace tare da nisantar dukkanin wani nau’in kayan maye saboda hakan ka iya sa rayuwarsu cikin halin ƙaƙani’kayi da lalacewar rayuwa, saboda hakan domin ganin sun inganta rayuwa to tabbas su tabbatar sun guji tare da nisantar kayan maye.

Domin ta’ammali da miyagun ƙwayoyi babu abin da yake jaza wa sai lalata rayuwa.

Tsofaffin
Wasu daga cikin shugabannin kungiyar tsofaffin daliban makarantar

Mataimakiyar shugaban kungiyar, Maryam Aminu Saulawa a jawabin da ta yi kira ga dalibai musamman mata akan muhimmancin ilimin ƴaƴa mata, inda ta jawo hankalinsu da su maida hankali akan karatunsu domin ganin sun cimma gaci a rayuwarsu ta nan gaba.

Ta yi kira ga ƴaƴa mata da su kuma tashi su nemi sana’a musamman ƙananan sana’o’i irin wanda mata ke iyayi a cikin gida ba tare da sun bar gidajen iyayansu ba, domin hakan zai taimaka wa rayuwar wajen ganin cewa sun dogara da kansu.

Wakilin shugabar makarantar malam Abubakar Sa’idu, ta nuna jin daɗinta bisa yadda daliban suka cimma nasara a rayuwarsu, da ya sanya suka waiwayo ƙannensu domin bada gudunmawarsu ga ci gaban makarantar.

Tsofaffin
Dalibai na sauraren lakca

Abubakar Sa’idu, ya ce makarantar tana alfahari da su kan wannan kyakkyawan aiki da suke yi, sai ya buƙace su da su ɗore da hakan domin cibgaban ilimi a makarantar da Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya, da kuma samar da al’umma tsaftatacciya.

A jawabinsu daban-daban uwar ƙungiyar Misis Fatima Abdullahi da Misis Hajara Korau da kuma malam Musa Umar sun jinjina wa tsofaffin daliban a bisa shirya wannan taro, inda suka bayyana cewa abubuwan da suka tattauna ya yi dai-dai da matsalolin da ake fuskanta a Jihar Katsina, wanda ake buƙatar gudunmuwar kowa a kan haka.

A jawabin skataren ƙungiyar, Sulaiman Nasir shi ma yayi kira ga daliban maza da mata da su maida hankali a karatunsu kuma su ƙauracewa duk wata hanya da ka iya jaza musu satar amsa a lokacin jarabawa, saboda hakan babbar illa ce ga ɗalibi mai neman ilimi.

Tsofaffin
Wasu daga cikin daliban da aka shirya wa lakca

Sakataren ƙungiyar ya kuma kara da cewa su tashi su nemi sana’a musamman maza, inda ya ce za su iya fara koyon aikin hannu misali: kafinta, kanikanci, fenti, gyaran wutar lantarki da dai sauransu, tun daga yanzu, wato tun suna da ƙuruciyarsu domin hakan zai taimaka musu, da kuma inganta rayuwarsu a shekaru masu zuwa.

Abdulrahman Ibrahim Hassan, jami’in hulda da jama’a na ƙungiyar, ya ce wannan shi ne karon farko da wannan ƙungiya ta shirya irin wannan taro domin ci gaban ɗalibai, ya kuma kara da cewa “In sha Allahu za mu ci gaba da aiwatar da dukkan kyawawan abubuwa ire-iren waɗannan domin ci gaban ɗalibai da matasa har ma da sauran al’umma.”

Daga ƙarshe, malamai da hukumar makarantar sun nuna jin daɗinsu akan irin wannan ci gaba da tsofaffin ɗalibanta suka kawo, sun kuma yi godiya tare da jaddada goyon bayansu akan dukkan abubuwa irin waɗannan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci Gaban MatasaKatsinaKungiyar Tsofaffin DalibaiLakcociMakaranta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tukunyar Gas Ta Yi Bindiga, Ta Yi Ajalin Wata Mata A Kwara

Next Post

Mutuwar Dan Davido: PDP Ta Dakatar Da Tarukan Siyasa A Jihar Osun

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

9 hours ago
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

9 hours ago
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

11 hours ago
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
Labarai

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

13 hours ago
Dawanau
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista

14 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

15 hours ago
Next Post
Mutuwar Dan Davido: PDP Ta Dakatar Da Tarukan Siyasa A Jihar Osun

Mutuwar Dan Davido: PDP Ta Dakatar Da Tarukan Siyasa A Jihar Osun

LABARAI MASU NASABA

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
jam'iyyu

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

June 13, 2025
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

June 13, 2025
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

June 13, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

June 13, 2025
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

June 13, 2025
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

June 13, 2025
Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

June 13, 2025
Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

June 13, 2025
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.