• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

by Abubakar Sulaiman
3 days ago
in Manyan Labarai
0
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an rundunar ƴansanda ta jihar Nasarawa sun samu nasarar cafke wani shahararren shugaban ƴan fashi da masu garkuwa da mutane, Mohammed Bammi wanda aka fi sani da Zomo, tare da wasu abokan aikinsa a yayin wani babban sumamen da suka kai kan miyagu a jihar.

Rundunar ta bayyana cewa Zomo ya daɗe yana jagorantar garkuwa da mutane da fashi a yankin ƙaramar hukumar Doma da kewaye. An cafke shi ne yayin wani sumamen tsaftace dajin Doka da jami’an sashin Doma suka gudanar, bayan ya tsere a watan Yuli. An ce ya yi yunƙurin kai wa jami’an hari da wuka lokacin da za a damƙe shi, amma aka rutsa shi aka kama shi da ransa.

  • Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano
  • Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa

Kakakin rundunar ƴansandan jihar, SP Ramhan Nansel, ya ce bincike ya kai jami’an zuwa maɓoyar Zomo a ƙauyen Alagye, Doma, inda suka gano makaman da suka haɗa da bindigar Pump Action, da bindigar AK-47 da aka haɗa ta a gida tare da mazaganya, da harsasai guda biyu da alburusai guda biyar, da wuka, da igiya, da wayoyi biyu, da kuma kayan sanya wa na jami’an NSCDC.

Haka kuma, Nansel ya ce jami’an rundunar Awe sun cafke wasu mutane biyar da ke cikin wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane 10 bayan samun sahihan bayanai. An kama su ne a ƙauyen Gidan Taku. Waɗanda aka cafke sun haɗa da Michael Ato, da Richard Ato, da Alom Bernard, da Hangior Ato da Jacob Hunde (wanda aka fi sani da Okocha). An kwace bindigogi biyu na AK-47 da aka yi a gida da harsashi guda daya daga hannunsu.

Kakakin ya ƙara da cewa bincike ya gano cewa a watan Afrilu 2024 wannan ƙungiya ta taɓa sace mijin Blessing John, mai suna John Ada Kuje, inda suka karɓi kuɗin fansa kafin su sake shi. Kwamishinan ƴansanda na jihar, CP Shetima Jauro Mohammed, ya jinjinawa jami’an bisa kwazo da sadaukarwa tare da jan hankalinsu da su ci gaba da matsa lamba har sai an kawar da masu garkuwa da mutane da ƴan fashi a jihar. Duk waɗanda aka kama an mika su ga sashi na musamman na masu garkuwa da mutane domin ƙarin bincike da gurfanarwa a kotu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NassarawaƳansanda
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Next Post

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Related

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 
Manyan Labarai

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

7 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Manyan Labarai

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

11 hours ago
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

13 hours ago
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar
Manyan Labarai

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

14 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

1 day ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Manyan Labarai

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

1 day ago
Next Post

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 27, 2025
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

August 27, 2025
Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

August 27, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.