ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Sin

Abiola Issah ita ce matukiyar jirgin kasa ta farko a kasar Nijeriya. A shekarar 2013, ta shiga shirin bayar da horo da kamfanin CCECC na kasar Sin ya shirya game da guraben aikin yi da za a samar ga al’ummar Nijeriya wajen gudanar da layin dogo na birnin Abuja, wanda kamfanin ya dauki nauyin ginawa. Bayan tsawon shekaru biyar, Abiola ta zama matukiyar jirgin kasa ta farko a kasar Nijeriya, har ma tsohon shugaban kasar marigayi Muhammadu Buhari ya gana da ita. Abiola ta ce, kamar sauran mutane irinta da dama, wannan layin dogo ya canja rayuwarta, ta ce, “sufuri ya zama tushen ci gaban kasa. Hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin a fannin sufuri, ba kawai ya inganta ababen more rayuwar kasashen ba, ya kuma farfado da tattalin arzikinsu da kuma samar da guraben ayyuka ga al’ummarsu. Matasa irina mun koyi fasahohi har ma mun samu ayyukan yi.”

 

Abin da ya faru ga malama Abiola kyakkyawan misali ne da ya shaida yadda ci gaban kasa ya taimaka ga inganta hakkin dan Adam, wato manyan ababen more rayuwa sun sa kaimin bunkasuwar tattalin arzikin kasa, tare da samar da guraben ayyukan yi ga al’ummarta, kuma ta hakan an kyautata rayuwar al’umma, baya ga karewa da inganta hakkin dan Adam.

ADVERTISEMENT

 

Ke nan hakkin rayuwa da kuma hakkin ci gaba sun kasance na farko daga cikin hakkokin dan Adam. Idan babu ci gaban kasa, babu tushen sauran hakkokin dan Adam ke nan. A don haka ne, a gun taron kara wa juna sani tsakanin Sin da kasashen Afirka kan hakkin dan Adam karo na farko da aka gudanar kwanan baya a birnin Addis Ababa, mahalarta taron sama da 200 da suka zo daga kasashen Sin da Afirka kimanin 44, suka yi musayar ra’ayoyi game da batun “hakkin samun ci gaba”. Matsayar da aka cimma a wajen taron ta kuma yi nuni da cewa, ci gaban kasa tushe ne na warware dukkanin matsalolin hakkin dan Adam.

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

 

A hakika, kwarewar kasar Sin a fannin inganta hakkin dan Adam ta hanyar raya ci gaban kasa, tana da muhimmiyar ma’ana ga kasashen Afirka wajen fid da kansu daga kangin talauci da kuma tabbatar da hakkin dan Adam. A game da hakan, Prof. Melha Rout Biel, shehun malami a cibiyar nazarin tsare-tsare da manufofi ta kasar Sudan ta Kudu ya yi nuni da cewa, “Kasashen Afirka da Sin dukkansu sun taba fuskantar koma baya sakamakon katsalandan da wasu kasashen suka yi musu. Batun hakkin ci gaba da kasar Sin ke magana a kai, abu ne da ya faru gare mu, don haka, muke goyon bayan kasar Sin wajen kokarin tabbatar da hakkinmu na ci gaba.”

 

Har kullum, kasar Sin na dukufa a kan “inganta hakkin dan Adam ta hanyar raya ci gaban kasa”, ta kuma gabatar da shawarar raya kasashen duniya, don “kar a bar wata kasa a baya”, kuma ta hanyar inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka a wannan fannin tare da cimma kyawawan nasarori. Misali kasar Sin ta taimaka wajen horar da dimbin kwararru na kasashen Afirka, don inganta kwarewar kasashen wajen tabbatar da ci gabansu. A kwanan nan, layin dogon Mombasa zuwa Nairobi da kamfanin kasar Sin ya gina ya cika kwanaki 3000 da fara aiki, wanda ya rage kudaden jigilar kayayyaki kimanin kaso 40% ga al’ummar wurin, tare da samar musu guraben aikin yi dubu 74, kuma hakan ya tabbatar da hakkin ci gaban al’ummar kasar. Har wa yau, Kasar Sin ta kuma yi gine-ginen ababen samar da makamashi mai tsabta sama da 100 a Afirka, ciki har da tashar samar da lantarki daga karfin ruwa ta Zungeru, wadanda suka samar da karfi ga kasashen Afirka wajen tabbatar da dauwamammen ci gabansu.

 

Duk da haka, kasashen yamma sun sha yin amfani da batun hakkin dan Adam a matsayin makami wajen tsoma baki cikin harkokin gidan kasashe masu tasowa. A Afirka, kasashen yamma su kan bayar da gudummawar tattalin arziki bisa gindaya sharuda kan batutuwan hakkin dan Adam, sai dai irin katsalandan da suke yi ta fakewa da batun hakkin dan Adam kan haifar da munanan illoli ga kare hakkin dan Adam a kasashen Afirka. Don haka, a matsayar da aka cimma a gun taron, Sin da kasashen Afirka sun jaddada cewa, suna goyon bayan kasa da kasa su zabi hanyar da ta dace da yanayin da suke ciki, kuma suna masu adawa da siyasantar da batun hakkin dan Adam ko kuma mai da shi tamkar makami.

 

A yayin da malama Abiola Issah ke samun horo a kasar Sin, ta taba shiga jirgin kasa mai saurin tafiya na kasar. Ta ce ba ta taba ganin jirgi mai sauri haka ba, kuma fatan ta shi ne, wata rana Nijeriya ma ta samu irin jirgin, kuma ta zama matukiya ta farko ta irin wannan jirgin kasa a gida Nijeriya. A ganina, yayin da ake aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya, tare da tabbatar da sakamakon da aka cimma a gun taron dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, burinta zai cika nan bada jimawa ba, kuma Sin da kasashen Afirka za su tabbatar da ci gabansu na bai daya bisa hadin gwiwarsu, a yayin da za su dada kyautata rayuwar al’ummunsu da kuma kara inganta hakkin dan Adam bisa ci gaban kasashensu.

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B
  • Sulaiman
    CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare
  • Sulaiman
    Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.