• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Shekara 13 Ya Kashe Kansa Bayan Jami’an Tsaro Sun Azabtar Da shi

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Tsaro
0
Ɗan Shekara 13 Ya Kashe Kansa Bayan Jami’an Tsaro Sun Azabtar Da shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani yaro mai shekaru 13 mai suna Wisdom Hashimu ya mutu ta hanyar rataye kansa a Unguwar Maigero da ke Karamar Hukumar Chikun a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne bayan wani soja da jami’an rundunar hadin gwiwa ta Cibilian Task Force a yankin sun azabtar da marigayin.

  • Sojoji Sun Kashe Boko Haram 4 A Borno
  • Boko Haram Sun Sace Fasinjoji A Kan Hanyar Maiduguri Zuwa Kano

Marigayi Wisdom wadda ta aikata wannan aika-aika a harabar gidan da ke kan titin Lafiya Sarki an ce an zarge shi da laifin satar Naira 10,000 daga wata makwabciyarsu a ranar.

A wani rahoto da gidan Talabijin na Channels TB ta fitar, makwabciyarta mai shekaru 16 mai suna Hope, an ce ta gayyaci saurayinta mai suna Segun Samson, wanda soja ne a sansanin Bodi da ke Fatakwal, babban birnin jihar Ribers wanda ya shiga cikin maganar.

Sai dai an nemi kudi an rasa a lokacin ziyarar, wanda hakan ya sa Hope ta hada saurayin nata da Wisdom da kuma dan uwanta zuwa ofishin Cibilian JTF.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Wisdom wacce ke zana jarabawar Karamar Sakandare, an bayyana cewa wani soja da jami’an Cibilian JTF ne suka yi masa mugun duka.

Mahaifin Wisdom, Mista Saul, wanda ya zanta da manema labarai ya ce, “Maimakon su kai rahoto ga ‘yansanda, sai kawai sojan ya ja dan’uwan Wisdom da Hope, wadanda ake zargi da satar kudin zuwa ofishin cibilian JTF.

“A ofishin cibilian JTF, an yi wa Wisdom mugun duka har ya kasa tafiya. Ya koma gida inda aka fara kula da lafiyarsa.”

Sai dai kuma wani abin takaici da ya afku shi ne an tsinci gawar Wisdom ya rataye kansa a bayan gidansu.

Sai dai a yayin da yake magana cikin bacin rai, mahaifin ya ce ‘yan Cibilian JTF sun dauki doka a hannunsu ta hanyar azabtar da Wisdom.

“Amma, ni abin da tunanina ya bani, Cibilian JTF ne kawai suka lakada wa Wisdom duka har ta kai ga suma, yayin da kanin Hope ya tsira ya dawo gida.

“Bayan an yi mata tambayoyi a gida, kaninta Hope ya amsa laifin da ya aikata, bayan da aka gano Naira 9,000 a aljihunsa, ya ce ya riga ya kashe Naira 1,000,” a cewarsa.

Don haka dangin sun bukaci a yi adalci kan azabtarwa da ake zargin marigayi dansu wanda hakan ya kai ga kashe shi.

“Tun daga lokacin aka fara bincike. Kwamishinan ‘yansandan ya umarci sashen binciken manyan laifuka da ya dauki nauyin lamarin kuma duk wanda ke da hannu za a gurfanar da shi a gaban kotu domin tabbatar da adalci”

Wisdom da ke zana jarabawar karamar Sakandare, an bayyana cewa wani soja da jami’an Cibilian JTF ne suka yi masa mugun duka.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Mansir Hassan, ya ce an fara bincike kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramBornoCJTFMaiduguriTsaroZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

Next Post

Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

Related

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja
Tsaro

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

5 days ago
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
Tsaro

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

1 week ago
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

2 weeks ago
Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato
Tsaro

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

2 weeks ago
Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
Tsaro

Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina

3 weeks ago
Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona Gidaje
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona Gidaje

3 weeks ago
Next Post
Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.