ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Shekara 13 Ya Kashe Kansa Bayan Jami’an Tsaro Sun Azabtar Da shi

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Kashe

Wani yaro mai shekaru 13 mai suna Wisdom Hashimu ya mutu ta hanyar rataye kansa a Unguwar Maigero da ke Karamar Hukumar Chikun a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne bayan wani soja da jami’an rundunar hadin gwiwa ta Cibilian Task Force a yankin sun azabtar da marigayin.

  • Sojoji Sun Kashe Boko Haram 4 A Borno
  • Boko Haram Sun Sace Fasinjoji A Kan Hanyar Maiduguri Zuwa Kano

Marigayi Wisdom wadda ta aikata wannan aika-aika a harabar gidan da ke kan titin Lafiya Sarki an ce an zarge shi da laifin satar Naira 10,000 daga wata makwabciyarsu a ranar.

ADVERTISEMENT

A wani rahoto da gidan Talabijin na Channels TB ta fitar, makwabciyarta mai shekaru 16 mai suna Hope, an ce ta gayyaci saurayinta mai suna Segun Samson, wanda soja ne a sansanin Bodi da ke Fatakwal, babban birnin jihar Ribers wanda ya shiga cikin maganar.

Sai dai an nemi kudi an rasa a lokacin ziyarar, wanda hakan ya sa Hope ta hada saurayin nata da Wisdom da kuma dan uwanta zuwa ofishin Cibilian JTF.

LABARAI MASU NASABA

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Wisdom wacce ke zana jarabawar Karamar Sakandare, an bayyana cewa wani soja da jami’an Cibilian JTF ne suka yi masa mugun duka.

Mahaifin Wisdom, Mista Saul, wanda ya zanta da manema labarai ya ce, “Maimakon su kai rahoto ga ‘yansanda, sai kawai sojan ya ja dan’uwan Wisdom da Hope, wadanda ake zargi da satar kudin zuwa ofishin cibilian JTF.

“A ofishin cibilian JTF, an yi wa Wisdom mugun duka har ya kasa tafiya. Ya koma gida inda aka fara kula da lafiyarsa.”

Sai dai kuma wani abin takaici da ya afku shi ne an tsinci gawar Wisdom ya rataye kansa a bayan gidansu.

Sai dai a yayin da yake magana cikin bacin rai, mahaifin ya ce ‘yan Cibilian JTF sun dauki doka a hannunsu ta hanyar azabtar da Wisdom.

“Amma, ni abin da tunanina ya bani, Cibilian JTF ne kawai suka lakada wa Wisdom duka har ta kai ga suma, yayin da kanin Hope ya tsira ya dawo gida.

“Bayan an yi mata tambayoyi a gida, kaninta Hope ya amsa laifin da ya aikata, bayan da aka gano Naira 9,000 a aljihunsa, ya ce ya riga ya kashe Naira 1,000,” a cewarsa.

Don haka dangin sun bukaci a yi adalci kan azabtarwa da ake zargin marigayi dansu wanda hakan ya kai ga kashe shi.

“Tun daga lokacin aka fara bincike. Kwamishinan ‘yansandan ya umarci sashen binciken manyan laifuka da ya dauki nauyin lamarin kuma duk wanda ke da hannu za a gurfanar da shi a gaban kotu domin tabbatar da adalci”

Wisdom da ke zana jarabawar karamar Sakandare, an bayyana cewa wani soja da jami’an Cibilian JTF ne suka yi masa mugun duka.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Mansir Hassan, ya ce an fara bincike kan lamarin.

Kashe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Iran Ta Yi Wa Sansanonin Sojin Amurka 20 Mummunar Barna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta
Tsaro

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane
Manyan Labarai

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026
Next Post
Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

LABARAI MASU NASABA

NDC:Kwankwaso Na Shan Sukar Jama’a Kan Naɗa Ɗansa A Matsayin Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan Kano

NDC:Kwankwaso Na Shan Sukar Jama’a Kan Naɗa Ɗansa A Matsayin Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan Kano

June 17, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Ceto Manoma 7 Da Aka Sace, Sun Kwato Babura Daga Hannun ’Yan Bindiga A Sokoto

June 17, 2026
Sojoji Sun Ceto Sauran Mutane 4 Da Aka Sace Tare Da Marigayi Janar Rabe A Katsina

Sojoji Sun Ceto Sauran Mutane 4 Da Aka Sace Tare Da Marigayi Janar Rabe A Katsina

June 17, 2026
Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

June 17, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

June 17, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 17, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.