• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Takarar Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Ya Halarci Taron Masu Ruwa Da Tsaki Da Atiku

by Bello Hamza
3 years ago
in Siyasa
0
Ɗan Takarar Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Ya Halarci Taron Masu Ruwa Da Tsaki Da Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar gwamnan Jihar Zamfara a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP, Dr. Dauda Lawal ya halarci taron masu ruwa da tsaki na yankin Arewa maso Yamma.

Taron wanda aka gudanar yau Talata a dakin taro na Bristol dake Kano, ya samu halartar gabaɗaya ‘yan takarar gwamna daga jihohi bakwai na yankin.

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Gana Da Jonathan, Ya Nemi Ya Mara Masa Baya

 

A yayin taron, wanda ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya yi don gudanar da tattaunawa ta musamman da ‘yan takarar gwamna na jihohin Arewa maso Yamma da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP daga yankin. Tsohon mataimakin Shugaban Ƙasan kuma Wazirin Adamawa ya yi kira ga musamman ‘yan takarar gwamnan da su ci gaba da yin aiki don nasarar jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ya bayyana cewa, idan har PDP ta lashe zaɓen shugaban ƙasa wanda shi ne za a fara gudanarwa, toh babu makawa jam’iyyar za ta lashe sauran kujeru, kama daga na gwamna, sanata, da sauransu.

Da farkon fara taron dai an gabatar da mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na yankin Arewa maso Yamma, Alhaji Hayatu Gwarzo wanda ya yi maraba da baki tare da bayyana maƙasudin kiran wannan tattaunawa ta musamman.

Bayan nan an gabatar da ‘yan takarar gwamna daga jihohi bakwai na wannan yankin. Dakta Dauda Lawal daga Jihar Zamfara, Ashiru Isa Kudan daga Jihae Kaduna, Mustapha Sule Lamido daga Jihar Jigawa, Sadiƙ Walid aga Jihar Kano, Janar Aminu Bande daga Jihar Kebbi, Sa’idu Umar daga Jihar Sakkwato.

Ɗan takarar gwamna na Jihar Kaduna, Isa Ashiru Kudan ne ya yi jawabi a madadin ‘yan uwansa ‘yan takara daga waɗannan jihohin Arewa maso Yamma guda bakwai. Ya bayyana jin daɗinsu ga irin wannan muhimmin taro, wanda a cewarsa ya ƙara kusanto ‘yan takarar da ɗan takarar shugaban ƙasa, Atiku Abubakar.

Cikin jiga-jigai da suka halarci wannan taro akwai gwamnan Jihar Delta kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a PDP, Ifeanyi Okowa, gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal, shugaban jam’iyyar PDP ta ƙasa, Sanata Iyochia Ayu, tsohon mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo, tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, tsohon gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Shehu Shema da dai sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Gana Da Jonathan, Ya Nemi Ya Mara Masa Baya

Next Post

Hadarin Kwale-kwale: Mutum Biyu Sun Rasu, An Ceto Bakwai A Jigawa

Related

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar
Siyasa

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

12 hours ago
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

20 hours ago
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Manyan Labarai

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

22 hours ago
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

1 day ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

2 days ago
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 
Siyasa

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

3 days ago
Next Post
Hadarin Kwale-kwale: Mutum Biyu Sun Rasu, An Ceto Bakwai A Jigawa

Hadarin Kwale-kwale: Mutum Biyu Sun Rasu, An Ceto Bakwai A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.