• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ɗaukar Abdulkarim Daura Matsayin Mataimakin Gwamna Zai Kawo Wa APC Nasara A Katsina”

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
APC

An yi kira ga masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC na jihar Katsina da su yi karatun ta nutsu su sake tunani game da ɗaukar ɗan takarar mataimakin gwamnan jihar Katsina a zaɓen 2023 mai zuwa.

Wani matashi ɗan jami’yyar APC a garin Katsina Sule Dudu Kofar Marusa ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Katsina.

  • Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ondo

 

Abdulkarim Dauda Daura na ɗaya daga cikin mutane tara da suka shiga zaɓen fidda gwani amma bai samu nasara ba a ƙarƙashin jam’iyar APC a jihar Katsina.

Sule Dudu Kofar Marusa ya ce idan jami’yyar APC ya ɗauki Abdulkarim Dauda Daura a matsayin wanda zai yi wa ɗan takarar jam’iyyar APC mataimaki zai taimaka wajan shawo kan matsalar tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Ya kuma ƙara da cewa har yanzu wuri bai korewa jami’yyar APC ba kasancewar Abdulkarim Dauda Daura masanin tsaro ne duba da irin yanayin da jihar Katsina ta shiga akan halin rashin tsaro.

“Abdulkarim Dauda Daura masanin tsaro ne, wanda yanzu haka yana ƙasashen waje akan abinda ya shafi sha’anin tsaro a duniya, inda ya ziyarci Kasashen Mexico da France da Italy da sauran su” inji shi.

Matashin dai ya ƙara da cewa idan har Masari da Dikko Umar Raɗɗa da Jami’yyar APC suna son cin zaɓe to su jawo A.D Daura su bashi mataimaki gwamna domin samun nasara a zaɓen 2023.

Haka kuma Sule Dudu ya yi bayanin cewa A.D Daura yana da kyakkyawan tarihi a lokacin da ya yi aikin ɗan Sanda, ba a taɓa kama shi da cin amana ba, sannan ya samawa jama’a da dama aikin yi fiye da mutane dubu biyar (5,000)

Sule Dudu ya ce idan jami’yyar APC ta ɗauki Abdulkarim Dauda Daura mataimakin gwamna za su samu mafita kuma wuri bai kore ba, yana mai cewa hakan zai baiwa yankin Daura mai ƙananan hukumomi 12 kawo kuri’unsu fiye da kashi 75%

“Lallai ya kamata jami’yyar mu ta APC ta san cewa Annabi ya fako, ta sake tunani, ta yi abinda ya kamata, duba da cewa akwai wasu alƙawura da har yanzu bata cika ba, wanda idan ba a yi abinda ya kamata ba, za a yi samun matsala” inji Sule Dudu

Daga karshe ya yi kira ga jama’a da su ajiye siyasa gefe guda akan matsalar tsaro, saboda shi dai ɗan ta’adda baya da gwani kowa ɗauka yake, ba ruwan shi da ɗan APC ko ɗan PDP koma wace irin jami’yya kamawa yake.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Next Post
Wani Ya Yi Alkawarin Auren Matashiyar Da Aka Yi Wa Sanadin Rasa Kafa A Sakkwato

Wani Ya Yi Alkawarin Auren Matashiyar Da Aka Yi Wa Sanadin Rasa Kafa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025
Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Yadda Ake Miyar Margi

Yadda Ake Miyar Margi

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.