ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ɗaukar Abdulkarim Daura Matsayin Mataimakin Gwamna Zai Kawo Wa APC Nasara A Katsina”

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
APC

An yi kira ga masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC na jihar Katsina da su yi karatun ta nutsu su sake tunani game da ɗaukar ɗan takarar mataimakin gwamnan jihar Katsina a zaɓen 2023 mai zuwa.

Wani matashi ɗan jami’yyar APC a garin Katsina Sule Dudu Kofar Marusa ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Katsina.

  • Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Ondo

 

ADVERTISEMENT

Abdulkarim Dauda Daura na ɗaya daga cikin mutane tara da suka shiga zaɓen fidda gwani amma bai samu nasara ba a ƙarƙashin jam’iyar APC a jihar Katsina.

Sule Dudu Kofar Marusa ya ce idan jami’yyar APC ya ɗauki Abdulkarim Dauda Daura a matsayin wanda zai yi wa ɗan takarar jam’iyyar APC mataimaki zai taimaka wajan shawo kan matsalar tsaro.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

Ya kuma ƙara da cewa har yanzu wuri bai korewa jami’yyar APC ba kasancewar Abdulkarim Dauda Daura masanin tsaro ne duba da irin yanayin da jihar Katsina ta shiga akan halin rashin tsaro.

“Abdulkarim Dauda Daura masanin tsaro ne, wanda yanzu haka yana ƙasashen waje akan abinda ya shafi sha’anin tsaro a duniya, inda ya ziyarci Kasashen Mexico da France da Italy da sauran su” inji shi.

Matashin dai ya ƙara da cewa idan har Masari da Dikko Umar Raɗɗa da Jami’yyar APC suna son cin zaɓe to su jawo A.D Daura su bashi mataimaki gwamna domin samun nasara a zaɓen 2023.

Haka kuma Sule Dudu ya yi bayanin cewa A.D Daura yana da kyakkyawan tarihi a lokacin da ya yi aikin ɗan Sanda, ba a taɓa kama shi da cin amana ba, sannan ya samawa jama’a da dama aikin yi fiye da mutane dubu biyar (5,000)

Sule Dudu ya ce idan jami’yyar APC ta ɗauki Abdulkarim Dauda Daura mataimakin gwamna za su samu mafita kuma wuri bai kore ba, yana mai cewa hakan zai baiwa yankin Daura mai ƙananan hukumomi 12 kawo kuri’unsu fiye da kashi 75%

“Lallai ya kamata jami’yyar mu ta APC ta san cewa Annabi ya fako, ta sake tunani, ta yi abinda ya kamata, duba da cewa akwai wasu alƙawura da har yanzu bata cika ba, wanda idan ba a yi abinda ya kamata ba, za a yi samun matsala” inji Sule Dudu

Daga karshe ya yi kira ga jama’a da su ajiye siyasa gefe guda akan matsalar tsaro, saboda shi dai ɗan ta’adda baya da gwani kowa ɗauka yake, ba ruwan shi da ɗan APC ko ɗan PDP koma wace irin jami’yya kamawa yake.

APC
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro: Manoma Sun Koma Gonakinsu A Katsina – Dikko Radda
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yusuf Buhari Ya Halarci Zaɓen Fidda Gwani Na Sanatan Shiyyar Daura

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Wani Ya Yi Alkawarin Auren Matashiyar Da Aka Yi Wa Sanadin Rasa Kafa A Sakkwato

Wani Ya Yi Alkawarin Auren Matashiyar Da Aka Yi Wa Sanadin Rasa Kafa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.