• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Bindiga Sun Ƙone Gidaje Da Motoci, Sun Sace Mutane 50 A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
in Tsaro
0
Ƴan Bindiga Sun Ƙone Gidaje Da Motoci, Sun Sace Mutane 50 A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni daga garin Maidabino a ƙaramar hukumar Ɗanmusa da ke jihar Katsina sun bayyana cewa ‘yan bindiga sun kai mummunan harin wuce gona da iri tare da kashe mutum tara.

A daren jiya Asabar ne dai ‘yan bindiga ɗauke da muggan makamai suka dira ƙauyen Maidabino da misalin karfe 7:00 na dare har zuwa 2:30 suna barna da ta’asa.

  • Atiku Ya Ziyarci Buhari Da Sarkin Daura Da Kuma Sarkin Katsina
  • Tsaro: Gwamnoni Arewa Maso Yamma Za Su Yi Taro Domin Neman Mafita A Katsina

Kazalika maharan sun ƙone motoci guda 9 da gidaje guda huɗu sannan sun ɗauke mutane fiye da hamsin duk a cikin daren.

Majiyar Leadership Hausa ta tabbatar da cewa an ƙone fiye da shaguna 15 ciki harda shagon sayar da magunguna a cikin garin Maidabino a yayin kai wannan hari na ƙare dangi.

Ado Gambo Maidabino na ɗaya daga cikin waɗanda aka konewa shagon sayar da magunguna wato ƙyamis a garin kuma ya bayyana takaicinsa gane da wannan hari.

Labarai Masu Nasaba

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Yana mai roko Allah ya kawo ƙarshen wannan bala’i tare da fatan Allah ya maida masu da abin da suka rasa.

Wani daga cikin ta'asar da ƴan bindigar suka yi.
Wani daga cikin ta’asar da ƴan bindigar suka yi.

Ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ɗan Musa a majalisar dokokin jihar Katsina Aminu Sai Baba ya tabbatar da faruwar wannan lamari tare da yin Allah dai da kuma kira ga gwamnati ta kawo ɗauki na gaggawa.

Ya kuma ƙara da cewa tuni gwamanti ta amsa kiran su inda yanzu haka an riga an kai jami’an tsaro wannan yanki domin dawowa da zaman lafiya.

Idan za a iya tunawa yankin Ɗan Musa na ɗaya daga cikin ƙananan hukumomin da ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga ba dare ba rana.

A gobe litanin ne shugaban ƙasa Bola Ahmad Tunibu zai buɗe wani taro akan harkar tsaro da gwamnonin arewa maso yamma da hukumar UNDP suka shirya a Katsina domin shawo kan matsalar tsaro a yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yin Watsi Da Babakere Da Daina Cin Riba Daga Yake-Yake Mafita Ce Ta Warware Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Duniya

Next Post

Sin Da EU Sun Amince Da Tattaunawa Kan Yadda EU Take Binciken Kin Ba Da Tallafi Kan EVs Na Kasar Sin

Related

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara
Tsaro

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

14 hours ago
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
Tsaro

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

2 weeks ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Tsaro

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

4 weeks ago
Kotu
Tsaro

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

4 weeks ago
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
Tsaro

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

4 weeks ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

1 month ago
Next Post
Sin Da EU Sun Amince Da Tattaunawa Kan Yadda EU Take Binciken Kin Ba Da Tallafi Kan EVs Na Kasar Sin

Sin Da EU Sun Amince Da Tattaunawa Kan Yadda EU Take Binciken Kin Ba Da Tallafi Kan EVs Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.