• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
in Labarai
0
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ƴansandan Jihar Jigawa ta ce ta samu nasarar gano wata mota da aka sace, tare da cafke wani da ake zargi da aikata laifin, tare da cafke masu safarar ƙwayoyi a wasu ayyuka daban-daban a ƙoƙarinta na yaƙi da miyagun laifuka a faɗin jihar.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi a ɗutse, babban birnin Jihar Jigawa, jami’in hulda da jama’a na rundunar ƴansandan jihar, SP Shi’isu Adam, ya ce motar da aka sace, ƙirar Kia Sorento mai lamba GWL 225 BB, an gano ta ne bayan wani aikin haɗin gwiwa da jami’an leƙen asiri suka gudanar.

“Wadanda suka saci motar ba a tantance su ba, sun sato motar a kasuwar Gujungu da ke ƙaramar Hukumar Taura a ranar 14 ga Yuli, 2025,” in ji sanarwar.

  • Ƴansanda Sun Fara Bi Gida-Gida Don Ƙwato Kayan Da Aka Sace Yayin Zanga-Zanga A Kano
  • Ƴansanda Sun Dakile Hari, Sun Ceto Mutane A Abuja

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Nan take ƴansandan suka tura tawagar jami’an tsaro daga sashin kula da sa ido na reshen Gujungu, inda suka shiga aikin tare da fara gudanar da bincike mai zurfi, gami da daukar matakin gaggawa, da kuma yin amfani da bayanan sirri na al’umma, an yi nasarar gano motar tare da cafke su a ƙauyen Kanya Babba da ke ƙaramar Hukumar Babura.

Sai dai PPRO na Jigawa ya bayyana cewa wadanda ake zargin sun gudu ne bayan da suka samu labarin jami’an ƴansanda na biye da su, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin cafke su domin gurfanar da su a gaban kuliya. “Motar da aka ƙwato tun daga nan aka miƙa ta ga mai ita bayan an tabbatar da tasa ce,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

A wani samame kuma, ƴansanda sun kama wani da ake zargin barayin USB ne, tare da ƙwato kayayyakin da aka lalata, ciki har da wata mota da aka yi amfani da ita wajen gudanar da aikin ba bisa ƙa’ida ba, inda ya ƙara da cewa “an kama su ne biyo bayan bayanan sirri da aka samu a ranar 15 ga Yuli, 2025, da misalin ƙarfe 0300 na safe.”

Wanda ake zargin mai suna Abubakar Sadi mai shekaru 25 dan asalin Kofar Waika ta jihar Kano, an kama shi a wurin da lamarin ya faru, yayin da sauran wadanda ake zargin suka tsere cikin daji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JigawaPolice
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Next Post

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

Related

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

38 minutes ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

4 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

5 hours ago
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara
Tsaro

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

5 hours ago
Next Post
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

LABARAI MASU NASABA

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.