ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Jihar Jigawa ta ce ta samu nasarar gano wata mota da aka sace, tare da cafke wani da ake zargi da aikata laifin, tare da cafke masu safarar ƙwayoyi a wasu ayyuka daban-daban a ƙoƙarinta na yaƙi da miyagun laifuka a faɗin jihar.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi a ɗutse, babban birnin Jihar Jigawa, jami’in hulda da jama’a na rundunar ƴansandan jihar, SP Shi’isu Adam, ya ce motar da aka sace, ƙirar Kia Sorento mai lamba GWL 225 BB, an gano ta ne bayan wani aikin haɗin gwiwa da jami’an leƙen asiri suka gudanar.

“Wadanda suka saci motar ba a tantance su ba, sun sato motar a kasuwar Gujungu da ke ƙaramar Hukumar Taura a ranar 14 ga Yuli, 2025,” in ji sanarwar.

ADVERTISEMENT
  • Ƴansanda Sun Fara Bi Gida-Gida Don Ƙwato Kayan Da Aka Sace Yayin Zanga-Zanga A Kano
  • Ƴansanda Sun Dakile Hari, Sun Ceto Mutane A Abuja

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Nan take ƴansandan suka tura tawagar jami’an tsaro daga sashin kula da sa ido na reshen Gujungu, inda suka shiga aikin tare da fara gudanar da bincike mai zurfi, gami da daukar matakin gaggawa, da kuma yin amfani da bayanan sirri na al’umma, an yi nasarar gano motar tare da cafke su a ƙauyen Kanya Babba da ke ƙaramar Hukumar Babura.

Sai dai PPRO na Jigawa ya bayyana cewa wadanda ake zargin sun gudu ne bayan da suka samu labarin jami’an ƴansanda na biye da su, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin cafke su domin gurfanar da su a gaban kuliya. “Motar da aka ƙwato tun daga nan aka miƙa ta ga mai ita bayan an tabbatar da tasa ce,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

A wani samame kuma, ƴansanda sun kama wani da ake zargin barayin USB ne, tare da ƙwato kayayyakin da aka lalata, ciki har da wata mota da aka yi amfani da ita wajen gudanar da aikin ba bisa ƙa’ida ba, inda ya ƙara da cewa “an kama su ne biyo bayan bayanan sirri da aka samu a ranar 15 ga Yuli, 2025, da misalin ƙarfe 0300 na safe.”

Wanda ake zargin mai suna Abubakar Sadi mai shekaru 25 dan asalin Kofar Waika ta jihar Kano, an kama shi a wurin da lamarin ya faru, yayin da sauran wadanda ake zargin suka tsere cikin daji.

Ƴansanda
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

MASU ALAKA

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna
Manyan Labarai

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta
Manyan Labarai

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu
Manyan Labarai

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Next Post
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

LABARAI MASU NASABA

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna

June 8, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.