ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Jihar Jigawa ta ce ta samu nasarar gano wata mota da aka sace, tare da cafke wani da ake zargi da aikata laifin, tare da cafke masu safarar ƙwayoyi a wasu ayyuka daban-daban a ƙoƙarinta na yaƙi da miyagun laifuka a faɗin jihar.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi a ɗutse, babban birnin Jihar Jigawa, jami’in hulda da jama’a na rundunar ƴansandan jihar, SP Shi’isu Adam, ya ce motar da aka sace, ƙirar Kia Sorento mai lamba GWL 225 BB, an gano ta ne bayan wani aikin haɗin gwiwa da jami’an leƙen asiri suka gudanar.

“Wadanda suka saci motar ba a tantance su ba, sun sato motar a kasuwar Gujungu da ke ƙaramar Hukumar Taura a ranar 14 ga Yuli, 2025,” in ji sanarwar.

ADVERTISEMENT
  • Ƴansanda Sun Fara Bi Gida-Gida Don Ƙwato Kayan Da Aka Sace Yayin Zanga-Zanga A Kano
  • Ƴansanda Sun Dakile Hari, Sun Ceto Mutane A Abuja

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Nan take ƴansandan suka tura tawagar jami’an tsaro daga sashin kula da sa ido na reshen Gujungu, inda suka shiga aikin tare da fara gudanar da bincike mai zurfi, gami da daukar matakin gaggawa, da kuma yin amfani da bayanan sirri na al’umma, an yi nasarar gano motar tare da cafke su a ƙauyen Kanya Babba da ke ƙaramar Hukumar Babura.

Sai dai PPRO na Jigawa ya bayyana cewa wadanda ake zargin sun gudu ne bayan da suka samu labarin jami’an ƴansanda na biye da su, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin cafke su domin gurfanar da su a gaban kuliya. “Motar da aka ƙwato tun daga nan aka miƙa ta ga mai ita bayan an tabbatar da tasa ce,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

A wani samame kuma, ƴansanda sun kama wani da ake zargin barayin USB ne, tare da ƙwato kayayyakin da aka lalata, ciki har da wata mota da aka yi amfani da ita wajen gudanar da aikin ba bisa ƙa’ida ba, inda ya ƙara da cewa “an kama su ne biyo bayan bayanan sirri da aka samu a ranar 15 ga Yuli, 2025, da misalin ƙarfe 0300 na safe.”

Wanda ake zargin mai suna Abubakar Sadi mai shekaru 25 dan asalin Kofar Waika ta jihar Kano, an kama shi a wurin da lamarin ya faru, yayin da sauran wadanda ake zargin suka tsere cikin daji.

Ƴansanda
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja
Labarai

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

September 15, 2026
Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta
Labarai

Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

September 15, 2026
’Yan Ta’adda Sun Kai Wa Ƙauyuka 2 Hari A Adamawa
Labarai

Boko Haram Sun Kashe Mutane 4 Tare Da Ƙone Gidaje A Adamawa

September 15, 2026
Next Post
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

September 15, 2026
Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

September 15, 2026
’Yan Ta’adda Sun Kai Wa Ƙauyuka 2 Hari A Adamawa

Boko Haram Sun Kashe Mutane 4 Tare Da Ƙone Gidaje A Adamawa

September 15, 2026
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

September 15, 2026
Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

September 15, 2026
Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Arziƙin Dangote Ya Haura Dala Biliyan 50 Bayan Fara Sayar Da Hannun Jarin Matatarsa – Forbes

September 15, 2026
Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

September 14, 2026
Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

September 14, 2026
Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

September 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.