• English
  • Business News
Wednesday, June 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

by Muhammad
1 year ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu Dalibai biyu na Jami’ar Jihar Nasarawa, Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a lokacin da suke ƙoƙarin karbar kayan abinci da gwamnatin Jihar ta ba su a matsayin tallafi don rage radadin tsadar rayuwa da tabarbarewar tattalin arziki a Nijeriya.

Daliban da ba a bayyana sunayensu ba, sun rasu a safiyar yau Juma’a yayin karbar kayan abincin tallafin.

  • An Kama Mutum 10 Bisa Zargin Safarar Mutane A Jihar Nasarawa
  • Rundunar ‘Yansandan Jihar Nasarawa Ta Kama Kungiyar Da Ta Sace Kananan Yara 45 

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa daliban da abin ya shafa mata ne, ko da yake majiyar ta ce wasu da dama sun samu raunuka daban-daban a yayin da abun ya faru a wurin taron rabon kayan abincin.

Shugaban kungiyar daliban jihar Nasarawa, Yunusa Yusuf Baduku, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibitocin da ke kusa domin kula da lafiyarsu.

Sai dai Baduku bai iya tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba nan take.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

“Hakika abin da ya faru da safiyar yau a Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi, lamarin abun tausayi ne.

“Bayan shirin da muka yi na rabon kayan abinci ga daliban da za a yi a Jami’ar, kwatsam sai ga su (daliban) sun isa wurin da yawansu, suka kuma yi nasara kan jami’an tsaro da ke wurin.

“Sun kutsa kai cikin wurin da ake rabon, abin bakin ciki shi ne yawancin dalibanmu mata sun samu raunuka da dama, yayin da wasu kuma suka shanye saboda yawan jama’a da ke wurin rabo kayan tallafin.

“A yanzu haka ina cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke garin Keffi, inda muka kawo wasu dalibanmu domin ba su kulawar gaggawa, bazan iya tabbatar da alkaluman wadanda suka jikkata ba a halin yanzu, saboda wasunsu suna asibitin makarantar yayin da wasu kuma suna asibitin makarantar, wasu suna nan a FMC, Keffi suna karbar magani,” a acewarsa.

LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Abdullahi Sule ya kara raba kayan tallafi ga daliban manyan makarantun jihar.

Gwamnatin jihar ta fara rabon shinkafa mai nauyin kilogiram 7:5 ga dalibai da ke Lafia babban birnin jihar a ranar Talata.

An rawaito cewa, an kuma ba kowane dalibi kudi naira 5,000 wanda ya kai naira miliyan 35 tare da kayan abinci.

Daliban da suka amfana da rabon sun fito ne daga Jami’ar Tarayya ta Lafia, Isa Mustapha Agwai Polytechnic Lafia, Kwalejin Aikin Gona Kimiyya da Fasaha ta Lafiya da kuma Makarantar koyon aikin jinya da ungozoma ta Lafia.

Gwamna Sule ya yi alkawarin za a mika irin wannan tallafin ga wasu cibiyoyin da ke wajen babban birnin jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jami'ar Jihar NasarawaMutuNasarawaRasu
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kautal Hore, Bodejo A Gaban Kotu Kan Zargin Ta’addanci

Next Post

Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma

Related

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
Manyan Labarai

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

3 hours ago
Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

7 hours ago
PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran

10 hours ago
An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna
Manyan Labarai

An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna

11 hours ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

14 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu
Manyan Labarai

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

24 hours ago
Next Post
Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma

Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa - Ngelzarma

LABARAI MASU NASABA

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

June 18, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

June 18, 2025
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

June 18, 2025
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

June 18, 2025
“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

June 18, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

June 18, 2025
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

June 18, 2025
Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

June 18, 2025
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

June 18, 2025
Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.