Wata kotun majistare da ke Nomansland a Jihar Kano ta bayar da umarnin tsare wani matashi mai suna Umar Hisham Fagge, wanda aka fi sani da Tsulange a TikTok, bisa zargin aikata alfasha da saɓa wa ɗabi’un al’umma da kuma ƙa’idojin addini.
Mai shari’a Hadiza Muhammad Hassan ce ta bayar da umarnin a tsare shi a gidan gyaran hali har zuwa ranar 3 ga Yuli, 2025, domin ci gaba da bincike.
Tsulange ya gurfana a gaban kotu ne bayan hukumar tantance fina-finai ta jihar Kano ta kama shi bisa bidiyon barkwanci da ya ɗauka yana wanka a titi sanye da tufafin ciki na mata. Hukumar ta bayyana cewa wannan bidiyo ya saɓa wa tarbiyya da al’adun Musulunci da ake mutuntawa a jihar.
- NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano
- Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna
A cewar mai magana da yawun hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, hukumar ta ce bidiyon ya wuce gona da iri wajen cin mutuncin jama’a, kuma yana daga cikin alamomin taɓarɓarewar tarbiyya da ke yawaita a tsakanin masu amfani da kafafen sada zumunta.
Rahotanni sun nuna cewa Tsulange ya saba ɗaukar irin waɗannan bidiyo a manyan tituna, har yana hana ababen hawa wucewa. Rundunar Ƴansandan Kano ta taɓa yin gargaɗi ga masu ƙirƙirar bidiyon abin dariya da su daina toshe tituna don ɗaukar bidiyo.
Hukumar tantance fina-finai ta jihar, ƙarƙashin jagorancin Abba El-Mustapha, ta ce za ta ci gaba da sa ido tare da ɗaukar matakin shari’a kan duk wani da ya yi amfani da sunan barkwanci don yada abin da ya kira da “nishadi mai tada zaune tsaye.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp