• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kar A Maimaita Kuskuren Da Aka Taba Yi Shi A Baya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kar A Maimaita Kuskuren Da Aka Taba Yi Shi A Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Yau 30 ga watan Mayu, rana ce ta musamman, a shekaru 55 da suka wuce ne, Chukwuemeka Ojukwu, shugaban al’ummar Igbo ta Najeriya ya sanar da ballewar yankin kudu maso gabas daga kasar Najeriya, don kafa “jamhuriyar Biafra”, lamarin da ya ta da yakin basasa a kasar. An shafe tsawon shekaru 2 da rabi ana wannan yaki, wanda ya haddasa hasarar miliyoyin rayukan mutane. A karshe dai, gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi nasarar kare cikakken yankin kasar, sai dai kamar yadda shugaban gwamnatin soja na kasar na lokacin Yakubu Gowon ya fada, “Ba wanda ya ci nasara a wannan yaki.” Sa’an nan matsalar kabilanci da yakin ya haddasa, tana ci gaba da haifar da mummunan tasiri kan harkokin siyasa, da tattalin arizki, da zaman al’umma na kasar Najeriya, har zuwa yanzu.

Idan mun waiwayi tarihi, mu kan gano shisshigin kasashen waje a cikin yakin da ke janyo baraka ga kasa. Bayan barkewar yakin Biafra, daga cikin kasashen yammacin duniya, kasar Faransa ce ta fara sayar wa “jamhuriyar Biafra” da makamai tun farkon yakin, sa’an nan kasar Portugal ta ba ta damar yin amfani da cibiyar gyaran jiragen samanta. Bayan da Chukwuemeka Ojukwu ya yi amfani da batun tamowa da matsalar tarin yawan ‘yan gudun hijira wajen neman taimako daga kasashen yamma, karin kasashe masu kudi na yammacin duniya sun samar da tallafi ga “jamhuriyar Biafra”. Sai dai Ojukwu ya yi amfani da kudaden wajen neman samun karin makamai da sojojin haya, maimakon kai dauki ga mutanen da suke fama da yunwa. A karshe dai, shissigin da kasashen waje suka yi ya tsawaita lokacin yakin, da sanya jama’ar kasar Najeriya cikin dimbin wahalhalu, da asarar rayuka da dukiyoyinsu.

Duk da haka, har zuwa yanzu, wasu kasashe ba su canza al’adarsu ta son sanya hannu cikin harkokin cikin gida na sauran kasashe ba. Har ma su kan fake da batun “hakkin dan Adam” da “dimokuradiya” da “ ‘yanci”, suna neman tabbatar da moriyar kai, yayin da suke yin shisshigi a wurare daban daban. Makarkashiyar da suka kulla ta jefa kasashe irinsu Iraki, da Afghanistan, da Syria, da Libya, da sai sauransu, cikin yanayi na fuskantar ballewar kasa da rarrabuwar kan jama’a. Wadannan kasashe suna kallon duniya tamkar wani “fili na wasa”, kana “wasannin” da suke yi su kan haddasa hasarorin rayukan jama’ar sauran kasashe, da salwantar dukiyoyinsu.

Saboda haka, wani babban aiki dake gaban kasashe masu tasowa shi ne su kare mulkin kai da ‘yancin kansu, da kokarin tabbatar da dinkuwar kasa waje guda. Ya kamata su yi kokarin dakile ra’ayin ballewar kasa, da hana munanan ayyukan ‘yan aware, gami da hana sauran kasashe yin shisshigi cikin harkokin su na cikin gida. Ta haka ne kawai za a iya magance sake yin kuskure na neman ballewar wani yanki daga wata kasa, da samun rarrabuwar kawunan al’umma, wanda aka sha yin sa a tarihin dan Adam. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin Kasar Sin Na Bincike Da Sa Ido Kan Harkokin Kudi Ya Ba Da Tabbaci Kan Bunkasar Kasa Mai Inganci

Next Post

Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

Related

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

7 hours ago
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa
Daga Birnin Sin

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

15 hours ago
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba
Daga Birnin Sin

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

16 hours ago
Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sin Ya Cimma Nasarar Shimfida Layin Dogo Na Farko Dakon Kaya Mafiya Nauyi A Hamadar Afirka

17 hours ago
An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Layin Dogo Mai Saurin Gudu Na Duniya Karo Na 12 A Beijing

18 hours ago
Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Yi Aiki Da MDD Don Samar Da Jagorancin Duniya Mai Cike Da Adalci Da Daidaito

19 hours ago
Next Post
Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

LABARAI MASU NASABA

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.