• English
  • Business News
Wednesday, May 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kar A Maimaita Kuskuren Da Aka Taba Yi Shi A Baya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kar A Maimaita Kuskuren Da Aka Taba Yi Shi A Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

Yau 30 ga watan Mayu, rana ce ta musamman, a shekaru 55 da suka wuce ne, Chukwuemeka Ojukwu, shugaban al’ummar Igbo ta Najeriya ya sanar da ballewar yankin kudu maso gabas daga kasar Najeriya, don kafa “jamhuriyar Biafra”, lamarin da ya ta da yakin basasa a kasar. An shafe tsawon shekaru 2 da rabi ana wannan yaki, wanda ya haddasa hasarar miliyoyin rayukan mutane. A karshe dai, gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi nasarar kare cikakken yankin kasar, sai dai kamar yadda shugaban gwamnatin soja na kasar na lokacin Yakubu Gowon ya fada, “Ba wanda ya ci nasara a wannan yaki.” Sa’an nan matsalar kabilanci da yakin ya haddasa, tana ci gaba da haifar da mummunan tasiri kan harkokin siyasa, da tattalin arizki, da zaman al’umma na kasar Najeriya, har zuwa yanzu.

Idan mun waiwayi tarihi, mu kan gano shisshigin kasashen waje a cikin yakin da ke janyo baraka ga kasa. Bayan barkewar yakin Biafra, daga cikin kasashen yammacin duniya, kasar Faransa ce ta fara sayar wa “jamhuriyar Biafra” da makamai tun farkon yakin, sa’an nan kasar Portugal ta ba ta damar yin amfani da cibiyar gyaran jiragen samanta. Bayan da Chukwuemeka Ojukwu ya yi amfani da batun tamowa da matsalar tarin yawan ‘yan gudun hijira wajen neman taimako daga kasashen yamma, karin kasashe masu kudi na yammacin duniya sun samar da tallafi ga “jamhuriyar Biafra”. Sai dai Ojukwu ya yi amfani da kudaden wajen neman samun karin makamai da sojojin haya, maimakon kai dauki ga mutanen da suke fama da yunwa. A karshe dai, shissigin da kasashen waje suka yi ya tsawaita lokacin yakin, da sanya jama’ar kasar Najeriya cikin dimbin wahalhalu, da asarar rayuka da dukiyoyinsu.

Duk da haka, har zuwa yanzu, wasu kasashe ba su canza al’adarsu ta son sanya hannu cikin harkokin cikin gida na sauran kasashe ba. Har ma su kan fake da batun “hakkin dan Adam” da “dimokuradiya” da “ ‘yanci”, suna neman tabbatar da moriyar kai, yayin da suke yin shisshigi a wurare daban daban. Makarkashiyar da suka kulla ta jefa kasashe irinsu Iraki, da Afghanistan, da Syria, da Libya, da sai sauransu, cikin yanayi na fuskantar ballewar kasa da rarrabuwar kan jama’a. Wadannan kasashe suna kallon duniya tamkar wani “fili na wasa”, kana “wasannin” da suke yi su kan haddasa hasarorin rayukan jama’ar sauran kasashe, da salwantar dukiyoyinsu.

Saboda haka, wani babban aiki dake gaban kasashe masu tasowa shi ne su kare mulkin kai da ‘yancin kansu, da kokarin tabbatar da dinkuwar kasa waje guda. Ya kamata su yi kokarin dakile ra’ayin ballewar kasa, da hana munanan ayyukan ‘yan aware, gami da hana sauran kasashe yin shisshigi cikin harkokin su na cikin gida. Ta haka ne kawai za a iya magance sake yin kuskure na neman ballewar wani yanki daga wata kasa, da samun rarrabuwar kawunan al’umma, wanda aka sha yin sa a tarihin dan Adam. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin Kasar Sin Na Bincike Da Sa Ido Kan Harkokin Kudi Ya Ba Da Tabbaci Kan Bunkasar Kasa Mai Inganci

Next Post

Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

Related

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

10 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

11 hours ago
Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje

12 hours ago
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC

13 hours ago
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar Sin 

15 hours ago
CMG Ta Cimma Nasarar Gudanar Da Gasar Mutum-Mutumin Inji Ta Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

CMG Ta Cimma Nasarar Gudanar Da Gasar Mutum-Mutumin Inji Ta Kasa Da Kasa

15 hours ago
Next Post
Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

Sojoji Sun Koka Bisa Jinkirin Yanke wa Ƴan Ta’adda 1,450 Hukunci

May 28, 2025
Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

Kotu Ta Ci Tarar  El-Rufai Miliyan 900 Saboda Wani Laifi Da Ya Yi A 2019

May 28, 2025
An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

An Gudanar Da Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC Karo Na Farko

May 27, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wani Ɗan Bindiga, Sun Ƙwato Makamai Bayan Artabu A Taraba

May 27, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

May 27, 2025
Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje

Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje

May 27, 2025
Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona 

Yamal Ya Saka Hannu A Sabon Kwantiragin Shekaru 6 A Barcelona 

May 27, 2025
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Ina Fatan Cigaba Da Taka Leda Har Zuwa Lokacin da Zan Cika Shekara 40 A Duniya – Salah

May 27, 2025
Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji

Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji

May 27, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC

May 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.