ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kar A Maimaita Kuskuren Da Aka Taba Yi Shi A Baya

by CMG Hausa
4 years ago

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Yau 30 ga watan Mayu, rana ce ta musamman, a shekaru 55 da suka wuce ne, Chukwuemeka Ojukwu, shugaban al’ummar Igbo ta Najeriya ya sanar da ballewar yankin kudu maso gabas daga kasar Najeriya, don kafa “jamhuriyar Biafra”, lamarin da ya ta da yakin basasa a kasar. An shafe tsawon shekaru 2 da rabi ana wannan yaki, wanda ya haddasa hasarar miliyoyin rayukan mutane. A karshe dai, gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi nasarar kare cikakken yankin kasar, sai dai kamar yadda shugaban gwamnatin soja na kasar na lokacin Yakubu Gowon ya fada, “Ba wanda ya ci nasara a wannan yaki.” Sa’an nan matsalar kabilanci da yakin ya haddasa, tana ci gaba da haifar da mummunan tasiri kan harkokin siyasa, da tattalin arizki, da zaman al’umma na kasar Najeriya, har zuwa yanzu.

Idan mun waiwayi tarihi, mu kan gano shisshigin kasashen waje a cikin yakin da ke janyo baraka ga kasa. Bayan barkewar yakin Biafra, daga cikin kasashen yammacin duniya, kasar Faransa ce ta fara sayar wa “jamhuriyar Biafra” da makamai tun farkon yakin, sa’an nan kasar Portugal ta ba ta damar yin amfani da cibiyar gyaran jiragen samanta. Bayan da Chukwuemeka Ojukwu ya yi amfani da batun tamowa da matsalar tarin yawan ‘yan gudun hijira wajen neman taimako daga kasashen yamma, karin kasashe masu kudi na yammacin duniya sun samar da tallafi ga “jamhuriyar Biafra”. Sai dai Ojukwu ya yi amfani da kudaden wajen neman samun karin makamai da sojojin haya, maimakon kai dauki ga mutanen da suke fama da yunwa. A karshe dai, shissigin da kasashen waje suka yi ya tsawaita lokacin yakin, da sanya jama’ar kasar Najeriya cikin dimbin wahalhalu, da asarar rayuka da dukiyoyinsu.

Duk da haka, har zuwa yanzu, wasu kasashe ba su canza al’adarsu ta son sanya hannu cikin harkokin cikin gida na sauran kasashe ba. Har ma su kan fake da batun “hakkin dan Adam” da “dimokuradiya” da “ ‘yanci”, suna neman tabbatar da moriyar kai, yayin da suke yin shisshigi a wurare daban daban. Makarkashiyar da suka kulla ta jefa kasashe irinsu Iraki, da Afghanistan, da Syria, da Libya, da sai sauransu, cikin yanayi na fuskantar ballewar kasa da rarrabuwar kan jama’a. Wadannan kasashe suna kallon duniya tamkar wani “fili na wasa”, kana “wasannin” da suke yi su kan haddasa hasarorin rayukan jama’ar sauran kasashe, da salwantar dukiyoyinsu.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, wani babban aiki dake gaban kasashe masu tasowa shi ne su kare mulkin kai da ‘yancin kansu, da kokarin tabbatar da dinkuwar kasa waje guda. Ya kamata su yi kokarin dakile ra’ayin ballewar kasa, da hana munanan ayyukan ‘yan aware, gami da hana sauran kasashe yin shisshigi cikin harkokin su na cikin gida. Ta haka ne kawai za a iya magance sake yin kuskure na neman ballewar wani yanki daga wata kasa, da samun rarrabuwar kawunan al’umma, wanda aka sha yin sa a tarihin dan Adam. (Bello Wang)

CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

Me Ya Sa Aka Ce Sin Ta Dauki Matakai Daidai Wajen Fama Da Cutar COVID-19?

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.