• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Sin 2022: Akwai Yiwar Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Fiye Yadda Ake Hasashe

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tattalin Arzikin Sin 2022: Akwai Yiwar Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Fiye Yadda Ake Hasashe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Masu azancin magana na cewa, “Juma’ar da za ta yi kyau, tun daga Laraba ake ganewa.” Da alama za mu iya cewa hasashen da masana suka yi game da yiwuwar samun tagomashin bunkasar tattalin arzikin kasar Sin ya fara tabbata, domin kuwa, a kwanakin baya bayan nan da suka gabata, dukkanin larduna da birane 31 na kasar Sin sun fitar da ma’aunin ci gaban tattalin arzikinsu na GDP a rubu’in farko na bana, inda alkaluma suka nuna cewa, sassa daban daban na kasar sun samu ci gaba mai inganci yadda ya kamata, duk da cewa ana fama da matsin lamba da sauye-sauyen yanayin da ake fuskanta na cikin gida da na kasa da kasa.

A cikin watanni uku na farkon bana, adadin GDP na larduna 11 da suka hada da lardin Guangdong ya zarta kudin Sin yuan triliyan daya, amma a makamancin lokacin bara, lardunan da adadin GDPn su ya zarta triliyan daya 8 ne kawai. Kana game da saurin ci gaban tattalin arzikin kuwa, ban da lardin Jilin wanda a baya bayan nan ya fuskantar tasirin yaduwar annobar COVID-19, sauran larduna da birane 30 dake fadin kasar sun samu karuwar tattalin arziki a rubu’in farkon bana, inda wasu lardunan dake tsakiya da yammacin kasar wadanda suka hada da Hubei da Shanxi da Xinjiang da Guizhou suka samu ci gaba cikin sauri har saurin ya kai kaso 6 bisa dari bisa makamancin lokacin bara.

Mataimakin shugaban cibiyar nazarin tattalin arziki bisa manyan tsare-tsare ta kasar Sin Wu Sa, ya bayyana a kwanan baya cewa, duk da cewa tattalin arzikin yankunan gabashin kasar ba su samu ci gaba cikin sauri ba, amma suna samun ci gaba mai inganci. Duk da barazana da kalubaloli daban daban da ta fuskanta, kasar Sin ta ci gaba da farfado da tattalin arzikinta. Kana ta cimma manyan manufofinta yadda ya kamata. Jimillar tattalin arzikin kasar Sin a bara ya kai dalar Amurka triliyan 3, wanda ba a taba ganin irinsa ba a tarihin duniya. Aiki ne mai wahala da kasar Sin ta kai ga cimma kyawawan sakamako. Hakan ya nuna cewa, kasar Sin na da karfin juriya wajen raya tattalin arziki, tana daidaita barazana yadda ya kamata, kana kuma hakan na da nasaba da yadda take yaki da annobar COVID-19, da kuma dora muhimmanci kan samun ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasa ba tare da tangarda ba.

Kasar Sin ta sanya burin daga yawan GDPn kasar da kaso 5.5 bisa dari a shekarar 2022. Ta yi tunani mai zurfi kan halin da take ciki a gida da waje ta fuskar bunkasa tattalin arziki, kana adadin ya dace da hakikanin yanayin bunkasar tattalin arziki. Dama dai masu hikimar magana na cewa, “Juma’ar da za ta yi kyau, daga Laraba ake ganewa.” (Ahmad Fagam)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanoni Masu Jarin Waje Dake Kasar Sin Na Kara Fadada Harkokinsu In Ji Sakamakon Wani Bincike

Next Post

Masana’antar Samar Da Kayayyaki Marasa Nauyi Ta Kasar Sin Ta Samu Tagomashi A Watanni 4 Na Farkon Bana

Related

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

43 minutes ago
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

18 hours ago
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya
Daga Birnin Sin

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

19 hours ago
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

20 hours ago
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

21 hours ago
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

22 hours ago
Next Post
Masana’antar Samar Da Kayayyaki Marasa Nauyi Ta Kasar Sin Ta Samu Tagomashi A Watanni 4 Na Farkon Bana

Masana’antar Samar Da Kayayyaki Marasa Nauyi Ta Kasar Sin Ta Samu Tagomashi A Watanni 4 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.