ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Sin 2022: Akwai Yiwar Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Fiye Yadda Ake Hasashe

by CMG Hausa
4 years ago

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Masu azancin magana na cewa, “Juma’ar da za ta yi kyau, tun daga Laraba ake ganewa.” Da alama za mu iya cewa hasashen da masana suka yi game da yiwuwar samun tagomashin bunkasar tattalin arzikin kasar Sin ya fara tabbata, domin kuwa, a kwanakin baya bayan nan da suka gabata, dukkanin larduna da birane 31 na kasar Sin sun fitar da ma’aunin ci gaban tattalin arzikinsu na GDP a rubu’in farko na bana, inda alkaluma suka nuna cewa, sassa daban daban na kasar sun samu ci gaba mai inganci yadda ya kamata, duk da cewa ana fama da matsin lamba da sauye-sauyen yanayin da ake fuskanta na cikin gida da na kasa da kasa.

A cikin watanni uku na farkon bana, adadin GDP na larduna 11 da suka hada da lardin Guangdong ya zarta kudin Sin yuan triliyan daya, amma a makamancin lokacin bara, lardunan da adadin GDPn su ya zarta triliyan daya 8 ne kawai. Kana game da saurin ci gaban tattalin arzikin kuwa, ban da lardin Jilin wanda a baya bayan nan ya fuskantar tasirin yaduwar annobar COVID-19, sauran larduna da birane 30 dake fadin kasar sun samu karuwar tattalin arziki a rubu’in farkon bana, inda wasu lardunan dake tsakiya da yammacin kasar wadanda suka hada da Hubei da Shanxi da Xinjiang da Guizhou suka samu ci gaba cikin sauri har saurin ya kai kaso 6 bisa dari bisa makamancin lokacin bara.

Mataimakin shugaban cibiyar nazarin tattalin arziki bisa manyan tsare-tsare ta kasar Sin Wu Sa, ya bayyana a kwanan baya cewa, duk da cewa tattalin arzikin yankunan gabashin kasar ba su samu ci gaba cikin sauri ba, amma suna samun ci gaba mai inganci. Duk da barazana da kalubaloli daban daban da ta fuskanta, kasar Sin ta ci gaba da farfado da tattalin arzikinta. Kana ta cimma manyan manufofinta yadda ya kamata. Jimillar tattalin arzikin kasar Sin a bara ya kai dalar Amurka triliyan 3, wanda ba a taba ganin irinsa ba a tarihin duniya. Aiki ne mai wahala da kasar Sin ta kai ga cimma kyawawan sakamako. Hakan ya nuna cewa, kasar Sin na da karfin juriya wajen raya tattalin arziki, tana daidaita barazana yadda ya kamata, kana kuma hakan na da nasaba da yadda take yaki da annobar COVID-19, da kuma dora muhimmanci kan samun ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasa ba tare da tangarda ba.

ADVERTISEMENT

Kasar Sin ta sanya burin daga yawan GDPn kasar da kaso 5.5 bisa dari a shekarar 2022. Ta yi tunani mai zurfi kan halin da take ciki a gida da waje ta fuskar bunkasa tattalin arziki, kana adadin ya dace da hakikanin yanayin bunkasar tattalin arziki. Dama dai masu hikimar magana na cewa, “Juma’ar da za ta yi kyau, daga Laraba ake ganewa.” (Ahmad Fagam)

CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Masana’antar Samar Da Kayayyaki Marasa Nauyi Ta Kasar Sin Ta Samu Tagomashi A Watanni 4 Na Farkon Bana

Masana’antar Samar Da Kayayyaki Marasa Nauyi Ta Kasar Sin Ta Samu Tagomashi A Watanni 4 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.