ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

12 Ga Yuni: Atiku, Tinubu Da Obi Da Ragowar Wasu Za Su Sanya Furanni A Kabarin Abiola

by Muhammad
4 years ago
12

‘Yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da takwaransa na Jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, a ranar Lahadi, 12 ga watan Yuni, 2022, jam’iyyar LP ta Peter Obi, da wasu fitattun ‘yan Najeriya da masu fafutukar tabbatar da dimokuradiyya za su ajiye furanni don tunawa da wanda ya lashe zaben shugaban kasa da aka soke ranar 12 ga watan Yunin 1993, marigayi Cif MKO Abiola.

Shugaban kwamitin shirya bikin ranar dimokradiyya na ranar 12 ga watan Yuni, Farfesa Anthony Kola ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.

  • Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP
  • Ni Zan Zaɓi Mataimakina Da Kaina – Tinubu

Ya ce, “A taron tunawa da zagayowar ranar dimokaradiyya na ranar 12 ga watan Yuni, wadda fitattun ‘yan uwa masu rajin kare dimokradiyya a Nijeriya suka kira, na sanar da cewa, ranar za ta karbi bakuncin fitattun ‘yan Nijeriya da masu fafutukar tabbatar da dimokuradiyya.

ADVERTISEMENT

A ranar Lahadi, 12 ga watan Yuni, 2022, a gidan MKO Abiola, wanda ya lashe zaben shugaban kasa na ranar 12 ga watan Yuni, 1993, wanda ya rasu a gidan yari saboda ya ki yin watsi da wa’adin tarihi da ‘yan Nijeriya suka ba shi kyauta.

“Wannan taron mai cike da tarihi wanda za a gudanar a harabar gidan MKO Abiola da ke Legas mai suna Cibiyar Dimokuradiyya ta Nijeriya ta kungiyar 12 ga watan Yuni, an yi shi ne da nufin tabbatar da amincewa da ranar 12 ga watan Yuni a matsayin ranar dimokuradiyyar Nijeriya a hukumance.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

“Don haka, ana sa ran taron mai cike da tarihi za a gudanar da addu’o’i da karramawa wasu da tunawa da ‘yan mazan jiya jarumai da jarumta a fannin dimokuradiyyar Nijeriya da kuma shimfida furen karramawa kan kabarin MKO Abiola domin tunawa da shi, da irin sadaukar da rayuwarsa mai daraja wajen kare hakkinsa.

Damar da al’umar Nijeriya suka ba shi a ranar 12 ga watan Yunin 1993 a lokacin haifuwar mulkin dimokaradiyya a Nijeriya.

“Wasu daga cikin jiga-jigan ‘yan Najeriya da aka gayyata don yin jawabai da karramawa a wajen taron mai taken ‘Fatan Zaben 93 da Yuni 12: Darasi don gudanar da sahihin Zabe a 2023’ su ne Farfesa Wole Soyinka, shugaban taron; Sanata Bola Ahmed Tinubu, da Waziri Atiku Abubakar da Peter Obi, Cif Ayo Adebanjo, Janar Alani Akinrinade, Farfesa Pat Utomi, Dr Olisa Agbakoba, Mr Femi Falana, Mr Mike Ozekhome, Dr Oby Ezekwesili, Sanata Shehu Sanni, Cif Dele Momodu da dai sauransu.

“Hakazalika, an yi gayyaci dukkan gwamnoni masu goyon bayan 12 ga watan Yuni da masu ruwa da tsaki domin su yi jawabi tare da nuna godiya a wajen taron tare da gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu a matsayin babban mai masaukin baki.”

12
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Next Post
2023: An Bukaci Tinubu Ya Dora Kan Irin Salon Mulkin Buhari Kwabo Da Kwabo

2023: An Bukaci Tinubu Ya Dora Kan Irin Salon Mulkin Buhari Kwabo Da Kwabo

LABARAI MASU NASABA

‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.