ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

by Muhammad
11 months ago
Shettima

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin da ke cewa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya kwatanta matakan da tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu suka ɗauka dangane da cire ko dakatar da gwamna a lokacin da suke kan mulkinsu ba. Ta ce irin waɗannan rahotanni ba gaskiya ba ne, kuma an kirkire su ne saboda a tayar da ƙurar siyasa.

A wata sanarwa da Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai a Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Stanley Nkwocha, ya fitar a ranar Jumma’a, an bayyana zargin a matsayin ƙarya mai cike da soki-burutsu, tare da musanta jita-jitar cewa Shettima ya soki Shugaba Tinubu dangane da rikicin siyasa da ya faru a Jihar Ribas.

  • Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 
  • Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

Sanarwar ta bayyana cewa jawaban da Mataimakin Shugaban Ƙasa ya yi a wajen ƙaddamar da littafin “OPL 245: The Inside Story of the $1.3 Billion Oil Block” wanda tsohon Antoni Janar na Tarayya, Mohammed Bello Adoke (SAN), ya rubuta, sun waiwaye ne kan tarihin baya saboda muhimmancin adana tarihin gwamnatoci, amma ba shi da alaƙa da sukar Shugaba Tinubu.

ADVERTISEMENT

“Wasu kafafen yaɗa labarai na yanar gizo da mutane sun juyar da kalaman Mataimakin Shugaban Ƙasa don cimma wata mummunar manufa,” cewar sanarwar. “Sun juya bayanin yadda gwamnatin Jonathan ta taɓa tunanin tsige Shettima daga matsayin gwamna a lokacin da rikicin Boko Haram ya yi tsanani.”

Sanarwar ta jaddada cewa Shettima yana bayar da labarin abubuwan da suka faru fiye da shekara goma da suka gabata, kuma ya yi haka don jinjina wa kyakkyawan halin Adoke a matsayin ma’aikacin gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Fadar Shugaban Ƙasa ta ce yunƙurin da aka yi na haɗa waɗannan maganganun da abubuwan da suka faru a Jihar Ribas, musamman batun dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara da ayyana dokar ta-baci, fassara ce da aka yi ta ba daidai ba, ko kuma suka ne ga kundin tsarin mulkin ƙasa.

“Domin kaucewa ruɗani, Shugaba Tinubu bai cire Gwamna Fubara daga mukaminsa ba,” sanarwar ta jaddada. “Abin da aka aiwatar dokar dakatarwa ce, ba tsige wa ba. Wannan mataki da kuma ayyana dokar ta-baci an ɗauke su ne sakamakon rikicin siyasa mai tsanani da ya faru a Jihar Ribas a wancan lokacin.”

Sanarwar ta ce rikicin da ya faru a Ribas ya cika sharuɗɗan da kundin tsarin mulki ya gindaya na ɗaukar matakan gaggawa, bisa tanadin Sashe na 305(3)(c), wanda ke bayar da damar hakan idan an samu rashin zaman lafiya da tsaro a matsayin matakin da ya zama wajibi a yi amfani da shi.

Shettima
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Rahotonni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
Labarai

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Next Post
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar 'Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.