• English
  • Business News
Sunday, June 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

15 Sun Mutu, 5 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi – FRSC 

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
15 Sun Mutu, 5 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi – FRSC 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC), ta tabbatar da mutuwar mutane 15 tare da jikkata wasu biyar a wani hatsarin mota da ya afku a Jihar Kogi.

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa hatsarin ya faru ne tsakanin J-5 Boxer bas da wata tankar mai, a Koton-Karfe kan babbar hanyar Lokoja zuwa Abuja da misalin karfe 7:30 na safiyar ranar Talata.

  • Ana Sa Ran Birtaniya Za Ta Fice Daga Tsibiran Malvinas Bayan Daidaita Ikon Mallakar Tsibiran Chagos
  • Man U Na Shirin Yin Wuf Da Giroud Don Maye Gurbin Ronaldo

Kwamandan FRSC a Kogi Stephen Dawulung, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce an garzaya da mutanen biyar da suka jikkata zuwa asibitin Ideal da ke Koton-Karfe domin ba su kulawar gaggawa.

Dawulung, ya ce an ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a dakin ajiye gawa na babban asibitin tarayya (FMC) da ke Lokoja.

Kwamandan sashen, ya bayyana cewa musabbabin hatsarin ya faru ne saboda keta dokokin hanya da direban motar bas din ya yi, wanda ya ke tukin mota a lokacin da ya ke kan hanyarsa ta zuwa Abuja daga Lokoja.

Labarai Masu Nasaba

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

“Direban bas din ya bar hannunsa yayin da yake tuki sai ya yi karo da wata motar dakon mai da ke zuwa.

“Alhamdulillahi motar dakon man fetur din ba ta tashi ba, da lamarin ya zama abun tashin hankali da damuwa.

“Abin takaicin shi ne, motar bas din tana dauke da tarkacen karfe da fasinjoji 17, 15 daga cikinsu an murkushe su kuma sun mutu a yayin da suka yi karo da juna.

“Abin takaici ne yadda ake cin zarafi da yawa da yadda ake karya dokar zirga-zirgar ababen hawa.

“Motocin da aka kebe don daukar kayayyaki ya kamata su dauki kaya kawai ba fasinjoji ba kamar yadda wannan lamari ya faru ” in ji Dawulung.

Sai dai kwamandan FRSC, ya jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, ya kuma shawarci masu ababen hawa da su rika bin ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa domin kaucewa hatsari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BasFRSCHatsarin MotaKogiTankar Man Fetur
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 4, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

Next Post

Kwalara Ta Kashe Mutane 620 A Malawi

Related

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
Manyan Labarai

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

9 hours ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

11 hours ago
Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
Labarai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

15 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Manyan Labarai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

16 hours ago
Tinubu
Labarai

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

16 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

17 hours ago
Next Post
Kwalara Ta Kashe Mutane 620 A Malawi

Kwalara Ta Kashe Mutane 620 A Malawi

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

June 14, 2025
Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

June 14, 2025
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

June 14, 2025
Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

June 14, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

June 14, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

June 14, 2025
Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

June 14, 2025
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

June 14, 2025
An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

June 14, 2025
Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.