• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

15 Sun Mutu, 5 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi – FRSC 

by Sadiq
3 years ago
Hatsarin Mota

Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC), ta tabbatar da mutuwar mutane 15 tare da jikkata wasu biyar a wani hatsarin mota da ya afku a Jihar Kogi.

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa hatsarin ya faru ne tsakanin J-5 Boxer bas da wata tankar mai, a Koton-Karfe kan babbar hanyar Lokoja zuwa Abuja da misalin karfe 7:30 na safiyar ranar Talata.

  • Ana Sa Ran Birtaniya Za Ta Fice Daga Tsibiran Malvinas Bayan Daidaita Ikon Mallakar Tsibiran Chagos
  • Man U Na Shirin Yin Wuf Da Giroud Don Maye Gurbin Ronaldo

Kwamandan FRSC a Kogi Stephen Dawulung, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce an garzaya da mutanen biyar da suka jikkata zuwa asibitin Ideal da ke Koton-Karfe domin ba su kulawar gaggawa.

Dawulung, ya ce an ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a dakin ajiye gawa na babban asibitin tarayya (FMC) da ke Lokoja.

Kwamandan sashen, ya bayyana cewa musabbabin hatsarin ya faru ne saboda keta dokokin hanya da direban motar bas din ya yi, wanda ya ke tukin mota a lokacin da ya ke kan hanyarsa ta zuwa Abuja daga Lokoja.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

“Direban bas din ya bar hannunsa yayin da yake tuki sai ya yi karo da wata motar dakon mai da ke zuwa.

“Alhamdulillahi motar dakon man fetur din ba ta tashi ba, da lamarin ya zama abun tashin hankali da damuwa.

“Abin takaicin shi ne, motar bas din tana dauke da tarkacen karfe da fasinjoji 17, 15 daga cikinsu an murkushe su kuma sun mutu a yayin da suka yi karo da juna.

“Abin takaici ne yadda ake cin zarafi da yawa da yadda ake karya dokar zirga-zirgar ababen hawa.

“Motocin da aka kebe don daukar kayayyaki ya kamata su dauki kaya kawai ba fasinjoji ba kamar yadda wannan lamari ya faru ” in ji Dawulung.

Sai dai kwamandan FRSC, ya jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, ya kuma shawarci masu ababen hawa da su rika bin ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa domin kaucewa hatsari.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Kwalara Ta Kashe Mutane 620 A Malawi

Kwalara Ta Kashe Mutane 620 A Malawi

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.