ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Akwai Yiwuwar Zagaye Na Biyu Idan Zaben Shugaban Kasa Bai Fitar Da Dan Takara Ba – INEC

by Sulaiman
3 years ago
INEC

Yayin da ta ke ta shirin gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na sanatoci, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta ce ta yi shirin gudanar da zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa a 2023 idan hakan ta kama.

 

Kakakin INEC Festus Okoye ne ya bayyana haka a wata ganawa da ya yi da editocin jaridu da wakilan kafafen yaɗa labarai a Abuja.

ADVERTISEMENT
  • 2023: INEC Ta Nemi Masu Kada Kuri’a Da Su Duba Sunayensu Cikin Wadanda Ta Yi Wa Rajista

Ya ce dama a bisa al’ada, INEC na yin irin wannan shiri a duk lokacin da za a yi zaɓen shugaban ƙasa, tun daga 1999.

 

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Okoye ya ce a irin wannan shiri, tun da farko dai INEC za ta ruɓanya adadin ƙuri’un da za ta buga. Wato idan masu zaɓe su miliyan 93, to INEC kan buga miliyan 186, ko da za a kai ga yin zagaye na biyu na zaɓen.

 

“Ana bugo ƙuri’un a lokaci ɗaya, saboda dokar ƙasa ta ce a yi zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa, idan a zagaye a farko aka kasa samun wanda ya yi nasara,” inji Okoye.

 

“Dalilin bugo su a lokaci ɗaya kuwa, saboda dokar ƙasa ta bayar da ratar kwanaki 21 kacal tsakanin ranar da aka yi zaɓen farko da kuma ranar da za a yi zagaye na biyu.”

 

Waɗanda Za Su Yi Zagaye Na Biyu:

INEC na shirya zaɓen shugaban ƙasa zagaye na biyu ne, “idan aka kasa samun wanda ya yi nasara a zagaye na farko.

INEC

“Dokar ƙasa ta ce tilas wanda zai yi nasara ya fi sauran ‘yan takara yawan ƙuri’u. Kuma tilas ya samu aƙalla kashi 1/4 na kashi 2 bisa bisa 3 na ƙuri’un da aka kaɗa a jihohi da FCT Abuja.

 

“‘Yan takara biyu ne za su iya shiga zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa, daga cikin jam’iyyu 18 da su ka shiga takara.

 

“Na farko shi ne wanda ya fi kowa yawan ƙuri’u, amma ya kasa samun aƙalla kashi 1/4 daga kashi 2 bisa 3 na yawan ƙuri’un jihohi da FCT Abuja.

 

“Sai kuma na biyun wanda zai yi zagaye na biyun ɗin, shi ne ya zo na biyu wajen samun kashi 1/4 na kashi 3 bisa 4 na ƙuri’un da aka kaɗa a jihohi da FCT Abuja.”

 

Okoye ya ƙara da kawo sashe na 134, ƙaramin sashe na 1 na Dokar Gwamnatin Tarayya, wanda ya wajibta sai wanda ya fi saura fifikon ƙuri’u ne za a ayyana cewa shi ya yi nasara.

 

Ya shaida cewa dukkan ƙuri’un da za a kaɗa da sauran kayan zaɓe su na ajiye a Babban Bankin Najeriya (CBN).

 

“Na’urar tantance adadin ƙuri’un da aka kaɗa da tantance masu zaɓe, wato BVAS ne kaɗai ba mu bai wa CBN ajiya ba. Wannan kuwa saboda su na da matuƙar muhimmancin da su na wajen mu, bisa tsauraran matakan kulawar ɓangarorin jami’an tsaro,” inji Okoye.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post
Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.