ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

by Leadership Hausa
4 years ago
Bullo

Mai bai wa shugaban kasa shawara ta fannin bunkasa zamantakewa, Miss Maryam Uwais ta bayyana cewa sakamakon karuwar yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya ya sa gwamnatin tarayya ta bullo da shirin tsamo yara daga hatsari (ARC-P).

Wannan shiri ne da zai magance matsalar da yara da kuma matasa suke fuskanta a dukkanin jihohin kasar nan ciki har da Babban Birnin Tarayya.

  • Mahara Sun Kashe ‘Yansanda 3 A Wani Hari Da Suka Kai Enugu
  • Peng Liyuan Ta Ziyarci Kwalejin Nazarin Kide-Kide Na Princess Galyani Vadana

Da take jawabi a wurin taron kara wa juna sani na kwanaki uku da za a horar da matasa har sama da 900 a Maiduguri da ke Jihar Borno, Misis Maryam wacce ta kasance jagorar shirin karkashin ofishin mataimakin shugaban kasa, ta bayyana cewa an samar da wannan shirin ne domin magance matsalolin da ke addabar yara da kuma matasa a fadin Nijeriya, wajen yin amfani da wasu matakai da suke da alaka da ilimi da lafiya da horar da sana’o’in da noma da kuwa wasanni.

ADVERTISEMENT

Misis Maryam wadda ta samu wakilcin mataimakin daraktar kasafi da tsare-tsare, Grace Akpabio ta ce za a gudanar da bayar da horon ga matasa a Jihar Borno har na tsawan makonni uku, domin samar musu da sana’o’in dogaro da kai.

A cewar mashawarciyar shugaban kasan, horar zai bunkasa basirar matasan wanda zai yi daidai da shirin ARC-P wajen tallafa wa rayuwarsu da kuma al’umma. Ta kara da cewa matasan da za su amfana da shirin suna da matukar rawar da za su taka wajen cimma nasarar wannan shirin wanda gwamnatin tarayya ta kaddamar tare da tallafin bangaren ‘yan kasuwa masu zaman kansu.

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

A nasa jawarin, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum ya yaba wa gwamnatin tarayya karkashin jagorancin APC na samar da shirin ARC-P. Ya ce a yanzu haka shirin yana gudana a kasa wanda zai shafe shekaru 25 yana gudana.

Zulum wanda ya samu wakilcin kwamishinan harkokin mata, Hajiya Zuwaira Gambo ya ce gwamnatin tarayya ta samar da shirye-shirye kamar irinsu ARC-P wadanda za su taimaka wajen magance matsalolin yara da matasa da mata musamman a yankin arewa maso yamma da yakin Boko Haram ya daidaita a tsawan shekari 12 da suka gabata.

Gwamna Zulum ya sha alwashin hada kai da tawagar shirin ARC-P wajen bayar da goyon baya domin shirin ya samu nasara, yayin da kuma ya yi kira ga matasan su jajirce wajen ganin sun amfanar da rayuwarsu kan wannan shirin.

Bullo
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81
Labarai

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa
Manyan Labarai

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya
Wasanni

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Next Post
FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Bullo

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.