ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

by Leadership Hausa
4 years ago
Bullo

Mai bai wa shugaban kasa shawara ta fannin bunkasa zamantakewa, Miss Maryam Uwais ta bayyana cewa sakamakon karuwar yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya ya sa gwamnatin tarayya ta bullo da shirin tsamo yara daga hatsari (ARC-P).

Wannan shiri ne da zai magance matsalar da yara da kuma matasa suke fuskanta a dukkanin jihohin kasar nan ciki har da Babban Birnin Tarayya.

  • Mahara Sun Kashe ‘Yansanda 3 A Wani Hari Da Suka Kai Enugu
  • Peng Liyuan Ta Ziyarci Kwalejin Nazarin Kide-Kide Na Princess Galyani Vadana

Da take jawabi a wurin taron kara wa juna sani na kwanaki uku da za a horar da matasa har sama da 900 a Maiduguri da ke Jihar Borno, Misis Maryam wacce ta kasance jagorar shirin karkashin ofishin mataimakin shugaban kasa, ta bayyana cewa an samar da wannan shirin ne domin magance matsalolin da ke addabar yara da kuma matasa a fadin Nijeriya, wajen yin amfani da wasu matakai da suke da alaka da ilimi da lafiya da horar da sana’o’in da noma da kuwa wasanni.

ADVERTISEMENT

Misis Maryam wadda ta samu wakilcin mataimakin daraktar kasafi da tsare-tsare, Grace Akpabio ta ce za a gudanar da bayar da horon ga matasa a Jihar Borno har na tsawan makonni uku, domin samar musu da sana’o’in dogaro da kai.

A cewar mashawarciyar shugaban kasan, horar zai bunkasa basirar matasan wanda zai yi daidai da shirin ARC-P wajen tallafa wa rayuwarsu da kuma al’umma. Ta kara da cewa matasan da za su amfana da shirin suna da matukar rawar da za su taka wajen cimma nasarar wannan shirin wanda gwamnatin tarayya ta kaddamar tare da tallafin bangaren ‘yan kasuwa masu zaman kansu.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

A nasa jawarin, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum ya yaba wa gwamnatin tarayya karkashin jagorancin APC na samar da shirin ARC-P. Ya ce a yanzu haka shirin yana gudana a kasa wanda zai shafe shekaru 25 yana gudana.

Zulum wanda ya samu wakilcin kwamishinan harkokin mata, Hajiya Zuwaira Gambo ya ce gwamnatin tarayya ta samar da shirye-shirye kamar irinsu ARC-P wadanda za su taimaka wajen magance matsalolin yara da matasa da mata musamman a yankin arewa maso yamma da yakin Boko Haram ya daidaita a tsawan shekari 12 da suka gabata.

Gwamna Zulum ya sha alwashin hada kai da tawagar shirin ARC-P wajen bayar da goyon baya domin shirin ya samu nasara, yayin da kuma ya yi kira ga matasan su jajirce wajen ganin sun amfanar da rayuwarsu kan wannan shirin.

Bullo
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

FERMA Ta Kammala Ayyukan Tituna 14 Don Saukaka Jigila Da Sufuri A Kebbi – Injiniya Rilwanu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.