ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Akwai Yiwuwar Zagaye Na Biyu Idan Zaben Shugaban Kasa Bai Fitar Da Dan Takara Ba – INEC

by Sulaiman
4 years ago
INEC

Yayin da ta ke ta shirin gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na sanatoci, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta ce ta yi shirin gudanar da zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa a 2023 idan hakan ta kama.

 

Kakakin INEC Festus Okoye ne ya bayyana haka a wata ganawa da ya yi da editocin jaridu da wakilan kafafen yaɗa labarai a Abuja.

ADVERTISEMENT
  • 2023: INEC Ta Nemi Masu Kada Kuri’a Da Su Duba Sunayensu Cikin Wadanda Ta Yi Wa Rajista

Ya ce dama a bisa al’ada, INEC na yin irin wannan shiri a duk lokacin da za a yi zaɓen shugaban ƙasa, tun daga 1999.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Okoye ya ce a irin wannan shiri, tun da farko dai INEC za ta ruɓanya adadin ƙuri’un da za ta buga. Wato idan masu zaɓe su miliyan 93, to INEC kan buga miliyan 186, ko da za a kai ga yin zagaye na biyu na zaɓen.

 

“Ana bugo ƙuri’un a lokaci ɗaya, saboda dokar ƙasa ta ce a yi zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa, idan a zagaye a farko aka kasa samun wanda ya yi nasara,” inji Okoye.

 

“Dalilin bugo su a lokaci ɗaya kuwa, saboda dokar ƙasa ta bayar da ratar kwanaki 21 kacal tsakanin ranar da aka yi zaɓen farko da kuma ranar da za a yi zagaye na biyu.”

 

Waɗanda Za Su Yi Zagaye Na Biyu:

INEC na shirya zaɓen shugaban ƙasa zagaye na biyu ne, “idan aka kasa samun wanda ya yi nasara a zagaye na farko.

INEC

“Dokar ƙasa ta ce tilas wanda zai yi nasara ya fi sauran ‘yan takara yawan ƙuri’u. Kuma tilas ya samu aƙalla kashi 1/4 na kashi 2 bisa bisa 3 na ƙuri’un da aka kaɗa a jihohi da FCT Abuja.

 

“‘Yan takara biyu ne za su iya shiga zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa, daga cikin jam’iyyu 18 da su ka shiga takara.

 

“Na farko shi ne wanda ya fi kowa yawan ƙuri’u, amma ya kasa samun aƙalla kashi 1/4 daga kashi 2 bisa 3 na yawan ƙuri’un jihohi da FCT Abuja.

 

“Sai kuma na biyun wanda zai yi zagaye na biyun ɗin, shi ne ya zo na biyu wajen samun kashi 1/4 na kashi 3 bisa 4 na ƙuri’un da aka kaɗa a jihohi da FCT Abuja.”

 

Okoye ya ƙara da kawo sashe na 134, ƙaramin sashe na 1 na Dokar Gwamnatin Tarayya, wanda ya wajibta sai wanda ya fi saura fifikon ƙuri’u ne za a ayyana cewa shi ya yi nasara.

 

Ya shaida cewa dukkan ƙuri’un da za a kaɗa da sauran kayan zaɓe su na ajiye a Babban Bankin Najeriya (CBN).

 

“Na’urar tantance adadin ƙuri’un da aka kaɗa da tantance masu zaɓe, wato BVAS ne kaɗai ba mu bai wa CBN ajiya ba. Wannan kuwa saboda su na da matuƙar muhimmancin da su na wajen mu, bisa tsauraran matakan kulawar ɓangarorin jami’an tsaro,” inji Okoye.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.