ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Akwai Yiwuwar Zagaye Na Biyu Idan Zaben Shugaban Kasa Bai Fitar Da Dan Takara Ba – INEC

by Sulaiman
4 years ago
INEC

Yayin da ta ke ta shirin gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na sanatoci, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta ce ta yi shirin gudanar da zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa a 2023 idan hakan ta kama.

 

Kakakin INEC Festus Okoye ne ya bayyana haka a wata ganawa da ya yi da editocin jaridu da wakilan kafafen yaɗa labarai a Abuja.

ADVERTISEMENT
  • 2023: INEC Ta Nemi Masu Kada Kuri’a Da Su Duba Sunayensu Cikin Wadanda Ta Yi Wa Rajista

Ya ce dama a bisa al’ada, INEC na yin irin wannan shiri a duk lokacin da za a yi zaɓen shugaban ƙasa, tun daga 1999.

 

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Okoye ya ce a irin wannan shiri, tun da farko dai INEC za ta ruɓanya adadin ƙuri’un da za ta buga. Wato idan masu zaɓe su miliyan 93, to INEC kan buga miliyan 186, ko da za a kai ga yin zagaye na biyu na zaɓen.

 

“Ana bugo ƙuri’un a lokaci ɗaya, saboda dokar ƙasa ta ce a yi zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa, idan a zagaye a farko aka kasa samun wanda ya yi nasara,” inji Okoye.

 

“Dalilin bugo su a lokaci ɗaya kuwa, saboda dokar ƙasa ta bayar da ratar kwanaki 21 kacal tsakanin ranar da aka yi zaɓen farko da kuma ranar da za a yi zagaye na biyu.”

 

Waɗanda Za Su Yi Zagaye Na Biyu:

INEC na shirya zaɓen shugaban ƙasa zagaye na biyu ne, “idan aka kasa samun wanda ya yi nasara a zagaye na farko.

INEC

“Dokar ƙasa ta ce tilas wanda zai yi nasara ya fi sauran ‘yan takara yawan ƙuri’u. Kuma tilas ya samu aƙalla kashi 1/4 na kashi 2 bisa bisa 3 na ƙuri’un da aka kaɗa a jihohi da FCT Abuja.

 

“‘Yan takara biyu ne za su iya shiga zagaye na biyu na zaɓen shugaban ƙasa, daga cikin jam’iyyu 18 da su ka shiga takara.

 

“Na farko shi ne wanda ya fi kowa yawan ƙuri’u, amma ya kasa samun aƙalla kashi 1/4 daga kashi 2 bisa 3 na yawan ƙuri’un jihohi da FCT Abuja.

 

“Sai kuma na biyun wanda zai yi zagaye na biyun ɗin, shi ne ya zo na biyu wajen samun kashi 1/4 na kashi 3 bisa 4 na ƙuri’un da aka kaɗa a jihohi da FCT Abuja.”

 

Okoye ya ƙara da kawo sashe na 134, ƙaramin sashe na 1 na Dokar Gwamnatin Tarayya, wanda ya wajibta sai wanda ya fi saura fifikon ƙuri’u ne za a ayyana cewa shi ya yi nasara.

 

Ya shaida cewa dukkan ƙuri’un da za a kaɗa da sauran kayan zaɓe su na ajiye a Babban Bankin Najeriya (CBN).

 

“Na’urar tantance adadin ƙuri’un da aka kaɗa da tantance masu zaɓe, wato BVAS ne kaɗai ba mu bai wa CBN ajiya ba. Wannan kuwa saboda su na da matuƙar muhimmancin da su na wajen mu, bisa tsauraran matakan kulawar ɓangarorin jami’an tsaro,” inji Okoye.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai
  • Sulaiman
    Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel
  • Sulaiman
    Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya
  • Sulaiman
    Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

MASU ALAKA

Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Labarai

Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

July 18, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
Next Post
Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

Fadar Shugaban Kasa Ta Bullo Da Shirin Ceto Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026
Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

July 18, 2026
Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026
Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

July 18, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.