• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: APC Ba Jam’iyyar Da Za A Goya Wa Baya Ba Ce, Sun Rusa Nijeriya – Atiku Ya Gargadi ‘Yan Nijeriya 

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
2023: APC Ba Jam’iyyar Da Za A Goya Wa Baya Ba Ce, Sun Rusa Nijeriya – Atiku Ya Gargadi ‘Yan Nijeriya 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, kuma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana jam’iyyar APC a matsayin wadanda suka rusa Nijeriya, ya kara da cewa basu cancanci a basu goyon baya ba. 

Atiku, ya bayyana hakan a lokacin da yake jawabi ga magoya bayan jam’iyyar a Benin, babban birnin Jihar Edo, a ranar Asabar a wajen taron gangamin jam’iyyarsa na shugaban kasa, ya bukaci jama’a su ci gaba da kasancewa masu biyayya ga PDP.

  • Kasar Sin Na Adawa Da Yin Shisshigi Cikin Harkokin Gidan Kasashe Masu Tasowa Bisa Hujjar Kare Hakkokin Dan Adam
  • Taron Wakilan Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Na 20 Da Muhimmancinsa

Ya ce jam’iyyar APC ta lalata tsarin ilimi, tattalin arziki, ababen more rayuwa da kuma kasa magance matsalolin tsaro da kasar nan ke fuskanta.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya kuma jaddada aniyarsa na magance matsalar rashin tsaro, inganta tattalin arziki, hada kan kasa da yaki da rashin tsaro.

Atiku ya ce “Mun yi alkawarin sake hade kasar nan. Me muke nufi da haka? Muna nufin za mu bai wa kowane bangare na kasar nan dama. Ba za a cire ku a cikin komai ba.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

“Na biyu, mun yi alkawarin dawo da tsaro. Za mu dawo da tsaro a kasar nan, ta yadda za ku yi tafiya dare da rana, domin ku je gonakinku, ta yadda za ku je ko’ina cikin tsari.

“Za mu sanya ‘yansanda da yawa a kan tituna. Za mu ba su kayan aiki; za mu karfafa musu kuma tun da mun yi alkawarin ba da karin iko ga jihohi da kananan hukumomi, za ku iya samun ‘yansanda na yankinku. Za mu tabbatar da cewa ‘yansandan yankinku ba su tursasa ku ba.

“Na uku, za mu mayar da dukkan yaranmu da suka cancanta makaranta. Dole ne su je makaranta; dole ne kowane yaro ya je makaranta.

“Idan za ku tuna, a shekarun PDP mun kafa ilimin firamare na tilas tun daga firamare zuwa sakandare kuma muna daukar nauyin ‘yan Nijeriya da su ilimantar da wadannan yara. Amma wannan gwamnati ba ta cika wannan alkawari ba. Mun yi muku alkawari; dole ne kowane yaro ya je makaranta kuma jami’o’inmu ba za su tafi yajin aiki ba.

“Haka kuma, mun yi alkawarin farfado da tattalin arzikin kasar nan. Za mu tabbatar da cewa masana’antunmu sun dawo da samar da kayayyaki a kasar nan. Za mu tabbatar da samar da isassun ayyukan yi ga matasanmu da ke fita waje makarantu. Wannan shi ne abin da muke nufi da farfado da tattalin arziki.

“Kun ga yadda APC ta lalata kasar nan, ta lalata tattalin arzikin kasar nan. Sun lalata damar karatunku. Sun lalata muku damar aikinku. APC ba jam’iyyar da za a goya wa baya ba ce. Sun lalata komai.

“Saboda haka, muna kira a gare ku da ku ci gaba da yin biyayya ga PDP kuma PDP za ta kasance mai biyayya gare ku.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuBeninEdoPDPTattalin ArzikiTsaroYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Rufe Babban Taron Wakilan Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Na 20

Next Post

Buhari Zai Tafi Koriya Ta Kudu Taron Lafiya Na Duniya Ranar Lahadi

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

4 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

4 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Buhari Zai Tafi Koriya Ta Kudu Taron Lafiya Na Duniya Ranar Lahadi

Buhari Zai Tafi Koriya Ta Kudu Taron Lafiya Na Duniya Ranar Lahadi

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.