• Leadership Hausa
Saturday, April 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: APC Ba Jam’iyyar Da Za A Goya Wa Baya Ba Ce, Sun Rusa Nijeriya – Atiku Ya Gargadi ‘Yan Nijeriya 

by Sadiq
5 months ago
in Siyasa
0
2023: APC Ba Jam’iyyar Da Za A Goya Wa Baya Ba Ce, Sun Rusa Nijeriya – Atiku Ya Gargadi ‘Yan Nijeriya 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, kuma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana jam’iyyar APC a matsayin wadanda suka rusa Nijeriya, ya kara da cewa basu cancanci a basu goyon baya ba. 

Atiku, ya bayyana hakan a lokacin da yake jawabi ga magoya bayan jam’iyyar a Benin, babban birnin Jihar Edo, a ranar Asabar a wajen taron gangamin jam’iyyarsa na shugaban kasa, ya bukaci jama’a su ci gaba da kasancewa masu biyayya ga PDP.

  • Kasar Sin Na Adawa Da Yin Shisshigi Cikin Harkokin Gidan Kasashe Masu Tasowa Bisa Hujjar Kare Hakkokin Dan Adam
  • Taron Wakilan Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Na 20 Da Muhimmancinsa

Ya ce jam’iyyar APC ta lalata tsarin ilimi, tattalin arziki, ababen more rayuwa da kuma kasa magance matsalolin tsaro da kasar nan ke fuskanta.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya kuma jaddada aniyarsa na magance matsalar rashin tsaro, inganta tattalin arziki, hada kan kasa da yaki da rashin tsaro.

Atiku ya ce “Mun yi alkawarin sake hade kasar nan. Me muke nufi da haka? Muna nufin za mu bai wa kowane bangare na kasar nan dama. Ba za a cire ku a cikin komai ba.

Labarai Masu Nasaba

Ku Dakata Da Gine-Gine A Filayen Gwamnati Da Makarantu – Abba Gida-Gida

Zababben Gwamnan Kano Ya Nada Sakataren Yada Labaransa

“Na biyu, mun yi alkawarin dawo da tsaro. Za mu dawo da tsaro a kasar nan, ta yadda za ku yi tafiya dare da rana, domin ku je gonakinku, ta yadda za ku je ko’ina cikin tsari.

“Za mu sanya ‘yansanda da yawa a kan tituna. Za mu ba su kayan aiki; za mu karfafa musu kuma tun da mun yi alkawarin ba da karin iko ga jihohi da kananan hukumomi, za ku iya samun ‘yansanda na yankinku. Za mu tabbatar da cewa ‘yansandan yankinku ba su tursasa ku ba.

“Na uku, za mu mayar da dukkan yaranmu da suka cancanta makaranta. Dole ne su je makaranta; dole ne kowane yaro ya je makaranta.

“Idan za ku tuna, a shekarun PDP mun kafa ilimin firamare na tilas tun daga firamare zuwa sakandare kuma muna daukar nauyin ‘yan Nijeriya da su ilimantar da wadannan yara. Amma wannan gwamnati ba ta cika wannan alkawari ba. Mun yi muku alkawari; dole ne kowane yaro ya je makaranta kuma jami’o’inmu ba za su tafi yajin aiki ba.

“Haka kuma, mun yi alkawarin farfado da tattalin arzikin kasar nan. Za mu tabbatar da cewa masana’antunmu sun dawo da samar da kayayyaki a kasar nan. Za mu tabbatar da samar da isassun ayyukan yi ga matasanmu da ke fita waje makarantu. Wannan shi ne abin da muke nufi da farfado da tattalin arziki.

“Kun ga yadda APC ta lalata kasar nan, ta lalata tattalin arzikin kasar nan. Sun lalata damar karatunku. Sun lalata muku damar aikinku. APC ba jam’iyyar da za a goya wa baya ba ce. Sun lalata komai.

“Saboda haka, muna kira a gare ku da ku ci gaba da yin biyayya ga PDP kuma PDP za ta kasance mai biyayya gare ku.”

Tags: APCAtikuBeninEdoPDPTattalin ArzikiTsaroYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Rufe Babban Taron Wakilan Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Na 20

Next Post

Buhari Zai Tafi Koriya Ta Kudu Taron Lafiya Na Duniya Ranar Lahadi

Related

Ku Dakata Da Gine-Gine A Filayen Gwamnati Da Makarantu – Abba Gida-Gida
Siyasa

Ku Dakata Da Gine-Gine A Filayen Gwamnati Da Makarantu – Abba Gida-Gida

21 hours ago
Zababben Gwamnan Kano Ya Nada Sakataren Yada Labaransa
Siyasa

Zababben Gwamnan Kano Ya Nada Sakataren Yada Labaransa

1 day ago
Abba Gida-Gida Ya Karbi Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Kano
Manyan Labarai

Abba Gida-Gida Ya Karbi Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Kano

3 days ago
Dubi Ga Amfanin Jajircewa A Gwagwarmayar Siyasa
Siyasa

Dubi Ga Amfanin Jajircewa A Gwagwarmayar Siyasa

6 days ago
Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa
Siyasa

Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

7 days ago
‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023
Siyasa

‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023

7 days ago
Next Post
Buhari Zai Tafi Koriya Ta Kudu Taron Lafiya Na Duniya Ranar Lahadi

Buhari Zai Tafi Koriya Ta Kudu Taron Lafiya Na Duniya Ranar Lahadi

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

March 31, 2023
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

March 31, 2023
Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

March 31, 2023
Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

March 31, 2023
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

March 31, 2023
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

March 31, 2023
Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

March 31, 2023
Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

March 31, 2023
Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

March 31, 2023
Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

March 31, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.