ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: APC Ba Jam’iyyar Da Za A Goya Wa Baya Ba Ce, Sun Rusa Nijeriya – Atiku Ya Gargadi ‘Yan Nijeriya 

by Sadiq
4 years ago
APC

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, kuma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana jam’iyyar APC a matsayin wadanda suka rusa Nijeriya, ya kara da cewa basu cancanci a basu goyon baya ba. 

Atiku, ya bayyana hakan a lokacin da yake jawabi ga magoya bayan jam’iyyar a Benin, babban birnin Jihar Edo, a ranar Asabar a wajen taron gangamin jam’iyyarsa na shugaban kasa, ya bukaci jama’a su ci gaba da kasancewa masu biyayya ga PDP.

  • Kasar Sin Na Adawa Da Yin Shisshigi Cikin Harkokin Gidan Kasashe Masu Tasowa Bisa Hujjar Kare Hakkokin Dan Adam
  • Taron Wakilan Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Na 20 Da Muhimmancinsa

Ya ce jam’iyyar APC ta lalata tsarin ilimi, tattalin arziki, ababen more rayuwa da kuma kasa magance matsalolin tsaro da kasar nan ke fuskanta.

ADVERTISEMENT

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya kuma jaddada aniyarsa na magance matsalar rashin tsaro, inganta tattalin arziki, hada kan kasa da yaki da rashin tsaro.

Atiku ya ce “Mun yi alkawarin sake hade kasar nan. Me muke nufi da haka? Muna nufin za mu bai wa kowane bangare na kasar nan dama. Ba za a cire ku a cikin komai ba.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Na biyu, mun yi alkawarin dawo da tsaro. Za mu dawo da tsaro a kasar nan, ta yadda za ku yi tafiya dare da rana, domin ku je gonakinku, ta yadda za ku je ko’ina cikin tsari.

“Za mu sanya ‘yansanda da yawa a kan tituna. Za mu ba su kayan aiki; za mu karfafa musu kuma tun da mun yi alkawarin ba da karin iko ga jihohi da kananan hukumomi, za ku iya samun ‘yansanda na yankinku. Za mu tabbatar da cewa ‘yansandan yankinku ba su tursasa ku ba.

“Na uku, za mu mayar da dukkan yaranmu da suka cancanta makaranta. Dole ne su je makaranta; dole ne kowane yaro ya je makaranta.

“Idan za ku tuna, a shekarun PDP mun kafa ilimin firamare na tilas tun daga firamare zuwa sakandare kuma muna daukar nauyin ‘yan Nijeriya da su ilimantar da wadannan yara. Amma wannan gwamnati ba ta cika wannan alkawari ba. Mun yi muku alkawari; dole ne kowane yaro ya je makaranta kuma jami’o’inmu ba za su tafi yajin aiki ba.

“Haka kuma, mun yi alkawarin farfado da tattalin arzikin kasar nan. Za mu tabbatar da cewa masana’antunmu sun dawo da samar da kayayyaki a kasar nan. Za mu tabbatar da samar da isassun ayyukan yi ga matasanmu da ke fita waje makarantu. Wannan shi ne abin da muke nufi da farfado da tattalin arziki.

“Kun ga yadda APC ta lalata kasar nan, ta lalata tattalin arzikin kasar nan. Sun lalata damar karatunku. Sun lalata muku damar aikinku. APC ba jam’iyyar da za a goya wa baya ba ce. Sun lalata komai.

“Saboda haka, muna kira a gare ku da ku ci gaba da yin biyayya ga PDP kuma PDP za ta kasance mai biyayya gare ku.”

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Buhari Zai Tafi Koriya Ta Kudu Taron Lafiya Na Duniya Ranar Lahadi

Buhari Zai Tafi Koriya Ta Kudu Taron Lafiya Na Duniya Ranar Lahadi

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.