ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: APC Ba Jam’iyyar Da Za A Goya Wa Baya Ba Ce, Sun Rusa Nijeriya – Atiku Ya Gargadi ‘Yan Nijeriya 

by Sadiq
4 years ago
APC

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, kuma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya bayyana jam’iyyar APC a matsayin wadanda suka rusa Nijeriya, ya kara da cewa basu cancanci a basu goyon baya ba. 

Atiku, ya bayyana hakan a lokacin da yake jawabi ga magoya bayan jam’iyyar a Benin, babban birnin Jihar Edo, a ranar Asabar a wajen taron gangamin jam’iyyarsa na shugaban kasa, ya bukaci jama’a su ci gaba da kasancewa masu biyayya ga PDP.

  • Kasar Sin Na Adawa Da Yin Shisshigi Cikin Harkokin Gidan Kasashe Masu Tasowa Bisa Hujjar Kare Hakkokin Dan Adam
  • Taron Wakilan Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Na 20 Da Muhimmancinsa

Ya ce jam’iyyar APC ta lalata tsarin ilimi, tattalin arziki, ababen more rayuwa da kuma kasa magance matsalolin tsaro da kasar nan ke fuskanta.

ADVERTISEMENT

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya kuma jaddada aniyarsa na magance matsalar rashin tsaro, inganta tattalin arziki, hada kan kasa da yaki da rashin tsaro.

Atiku ya ce “Mun yi alkawarin sake hade kasar nan. Me muke nufi da haka? Muna nufin za mu bai wa kowane bangare na kasar nan dama. Ba za a cire ku a cikin komai ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

“Na biyu, mun yi alkawarin dawo da tsaro. Za mu dawo da tsaro a kasar nan, ta yadda za ku yi tafiya dare da rana, domin ku je gonakinku, ta yadda za ku je ko’ina cikin tsari.

“Za mu sanya ‘yansanda da yawa a kan tituna. Za mu ba su kayan aiki; za mu karfafa musu kuma tun da mun yi alkawarin ba da karin iko ga jihohi da kananan hukumomi, za ku iya samun ‘yansanda na yankinku. Za mu tabbatar da cewa ‘yansandan yankinku ba su tursasa ku ba.

“Na uku, za mu mayar da dukkan yaranmu da suka cancanta makaranta. Dole ne su je makaranta; dole ne kowane yaro ya je makaranta.

“Idan za ku tuna, a shekarun PDP mun kafa ilimin firamare na tilas tun daga firamare zuwa sakandare kuma muna daukar nauyin ‘yan Nijeriya da su ilimantar da wadannan yara. Amma wannan gwamnati ba ta cika wannan alkawari ba. Mun yi muku alkawari; dole ne kowane yaro ya je makaranta kuma jami’o’inmu ba za su tafi yajin aiki ba.

“Haka kuma, mun yi alkawarin farfado da tattalin arzikin kasar nan. Za mu tabbatar da cewa masana’antunmu sun dawo da samar da kayayyaki a kasar nan. Za mu tabbatar da samar da isassun ayyukan yi ga matasanmu da ke fita waje makarantu. Wannan shi ne abin da muke nufi da farfado da tattalin arziki.

“Kun ga yadda APC ta lalata kasar nan, ta lalata tattalin arzikin kasar nan. Sun lalata damar karatunku. Sun lalata muku damar aikinku. APC ba jam’iyyar da za a goya wa baya ba ce. Sun lalata komai.

“Saboda haka, muna kira a gare ku da ku ci gaba da yin biyayya ga PDP kuma PDP za ta kasance mai biyayya gare ku.”

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Next Post
Buhari Zai Tafi Koriya Ta Kudu Taron Lafiya Na Duniya Ranar Lahadi

Buhari Zai Tafi Koriya Ta Kudu Taron Lafiya Na Duniya Ranar Lahadi

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.