• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: APC Da PDP Sun Riga Sun Yi Karfi Ita Kuma Jam’iyyar NNPP Na Kara Karfi –Rufa’i Alkali

Jam'iyyar zata ba da mamaki a duk fadin Nijeriya a babban zaben 2023, cewar Shugaban NNPP na kasa.

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
2023: APC Da PDP Sun Riga Sun Yi Karfi Ita Kuma Jam’iyyar NNPP Na Kara Karfi –Rufa’i Alkali
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar NNPP ta ce bata mance da karfin jam’iyyun PDP da APC ba amma tana gina shirye-shirye domin karawa da su.

tsohon mai baiwa tsohon shugaban kasa shawara kan harkokin siyasa, Goodluck Jonathan kuma Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Rufai Alkali, ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN a ranar Laraba a Legas.

  • 2023: A Shirye Muke Mu Bude Kofar Kulla Kawance Da Sauran Jam’iyyu Kafin Zabe –NNPP
  • Rikicin NNPP: Kwankwaso Ya Ci Amanarmu – Shekarau

Alkali, wanda ya taba zama tsohon sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, ya ce jam’iyyar NNPP zata ba da mamaki a fadin kasar nan a babban zaben 2023.

Ya ce irin shugabancin da jam’iyyar NNPP zata kawo a Nijeriya zai sha bamban da yadda sauran jam’iyyun siyasa suka bayar ko kuma suke bayarwa.

“Mun fito ne don rage ɓacin rai da fushi da ɗaci a cikin ƙasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

“NNPP jam’iyya ce da ta kafu da nufin zata kawo ci gaban Nijeriya.

“Yanzu mun samu ‘yan takararmu a matakai daban-daban kuma muna shirye-shiryen tunkarar yakin neman zabe nan ba da dadewa ba.

“Hakika, ba mu manta da karfi da tasirin da PDP da APC za su iya yi ba. Jam’iyyarmu tana kan hanya, muna da karfi sosai. Muna kara karfi. Mun shirya.

Shugaban wanda ya ce ‘yan Nijeriya na bukatar canji na gaskiya, ya ce jam’iyyar NNPP a shirye ta ke ta zaburar da jama’a domin gudanar da zabe a 2023.

Alkali ya yi nuni da cewa, kasashe da dama da ba su da dimbin albarkatu kamar yadda Nijeriya ta samu damar yin amfani da abinda ake da su don gina kasa.

Ya ce, ya kamata Nijeriya ta kasance daya daga cikin manyan kasashen nahiyar Afirka.

“’Yan Nijeriya na da burin ganin Nijeriya ta zama kasa mai inganci, ganin cewa mu ne mafi yawan al’ummar bakaken fata a nahiyar.

“Har ila yau, akwai tunanin cewa bayan shekaru 22 na mulkin dimokuradiyya, ya kamata kasar ta girma cikin nasara.

“A ka’ida, ya kamata mu yi nisa fiye da inda muke yanzu. Tsaro da tattalin arzikin al’umar kasar na fuskantar matsin lamba. A cewar Alkali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023AlkaliKwankwasoNNPP
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Da Alamun Tafka Magudi Ta Hanyar Amfani Da Na’urar Aike Da Sakamakon Zaɓe

Next Post

“Ba Zan Mara Wa Atiku Ko Wani Dan Takara Na Kyale Tinubu Ba” —Buhari

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

4 hours ago
2023
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

11 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

12 hours ago
Next Post
Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa

“Ba Zan Mara Wa Atiku Ko Wani Dan Takara Na Kyale Tinubu Ba” —Buhari

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
2023

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.