• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ba Mu Nada Janar Bamaiyi A Matsayin Daraktan Yakin Zaben PDP A Kebbi Ba – Jam’iyyar

by Sulaiman and Umar Faruk
3 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP a jihar Kebbi ta musanta nada Janar Ishaya Bamaiyi a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa Atiku Abubakar a yayin babban zaben 2023 da ke tafe.

Shugaban jam’iyyar a jihar, Alhaji Usman Bello-Suru, shi ne ya bayyana haka a Birnin Kebbi, babban birnin jihar yayin da yake mayar da martani ga wani rahoton yanar gizo da daya daga cikin jaridun nan kasa (Wacce ba namu ba) ta wallafa.

  • Jam’iyyar PDP A Kebbi Ta Shirya Tarbar Dan Takarar Shugaban Kasa, Atiku Abubakar

Wakilinmu LEADERSHIP ya ruwaito wannan labarin ya fito ne daga wani taron manema labarai da Alhaji Kabiru Tanimu-Turaki, Shugaban kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP (BOT) kuma tsohon ministan ayyuka na musamman ne ya bayar a baya.

Alhaji Bello-Suru ya ce: “Hankalin jam’iyyar PDP a jihar Kebbi ya karkata ne ga wata hira da aka wallafa da Alhaji Kabiru Tanimu Turaki (SAN) ya yi da manema labarai kuma jaridar ta buga a dandalinta na yanar gizo mai taken: “PDP ta nada Janar Bamaiyi Darakta Janar na yakin neman zaben Atiku Abubakar a shugaban kasa na Jihar Kebbi”.

“Tattaunawar da aka yi a kafafen yada labarai da ake magana a kai da jama’a musamman ‘ya’yan jam’iyyar PDP na jihar Kebbi aka nada Janar Ishaya Bamaiyi a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a jihar Kebbi.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Muna so mu bayyana cewa nadin ya wanzu ne kawai a cikin tunanin Kabiru Tanimu Tukari, SAN, amma ba da yawun Jam’iyyar a matakin jiha ko a Tarayya ba.”

Ya ce hakika an kafa kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa a jihar Kebbi kamar yadda shugabannin jam’iyyar na kasa suka bayar a wata daya da ya gabata, inda ya kara da cewa majalisar yakin neman zaben shugaban kasa tana karkashin jagorancin Dakta Bello Haliru, wanda shi ne tsohon shugaban Jam’iyyar PDP na kasa.

Shugaban ya ce bin umarnin hedkwatar kasa, “Duk jihar da ba jam’iyya ba ce, babban jigo a jam’iyyar ya zama shugaban kwamitin yakin neman zabe, yayin da mai rike da tuta na gwamna ya zama mataimakinsa, don haka Dakta Bello Haliru da Janar Aminu Bande mai ritaya su ne ke rike da Jagorancin shugabancin yakin neman zaben Shugaban kasa a Jihar.”

A cewarsa, Darakta Janar din jam’iyyar guda daya ne kawai, majalisar yakin neman zaben shugaban kasa, wanda shi ne Gwamna Aminu Tambuwal na Jihar Sakkwato, yayin da Jihohi ke da shugabanni ba Darakta Janar ba .

Daga karshe Alhaji Usman Bello-Suru ya yi kira ga jama’a da su yi watsi da labaran da aka wallafa a kafafen yada labarai, yana mai jaddada cewa PDP na nan daram a Jihar Kebbi domin kuwa Kabiru Tanimu-Turaki bai wakiltan kowa dangane da shugabanci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Buhari Zai Gabatar Da Kasafin Kudi Na N19.76tn Na 2023 A Majalisar Wakilai Ranar Juma’a

Za A Yi Wa 'Ƴan Siyasa Da Ma'aikatan Shari'a Ƙarin Albashi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.