• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ba Mu Nada Janar Bamaiyi A Matsayin Daraktan Yakin Zaben PDP A Kebbi Ba – Jam’iyyar

by Sulaiman and Umar Faruk
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Ba Mu Nada Janar Bamaiyi A Matsayin Daraktan Yakin Zaben PDP A Kebbi Ba – Jam’iyyar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP a jihar Kebbi ta musanta nada Janar Ishaya Bamaiyi a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa Atiku Abubakar a yayin babban zaben 2023 da ke tafe.

Shugaban jam’iyyar a jihar, Alhaji Usman Bello-Suru, shi ne ya bayyana haka a Birnin Kebbi, babban birnin jihar yayin da yake mayar da martani ga wani rahoton yanar gizo da daya daga cikin jaridun nan kasa (Wacce ba namu ba) ta wallafa.

  • Jam’iyyar PDP A Kebbi Ta Shirya Tarbar Dan Takarar Shugaban Kasa, Atiku Abubakar

Wakilinmu LEADERSHIP ya ruwaito wannan labarin ya fito ne daga wani taron manema labarai da Alhaji Kabiru Tanimu-Turaki, Shugaban kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP (BOT) kuma tsohon ministan ayyuka na musamman ne ya bayar a baya.

Alhaji Bello-Suru ya ce: “Hankalin jam’iyyar PDP a jihar Kebbi ya karkata ne ga wata hira da aka wallafa da Alhaji Kabiru Tanimu Turaki (SAN) ya yi da manema labarai kuma jaridar ta buga a dandalinta na yanar gizo mai taken: “PDP ta nada Janar Bamaiyi Darakta Janar na yakin neman zaben Atiku Abubakar a shugaban kasa na Jihar Kebbi”.

“Tattaunawar da aka yi a kafafen yada labarai da ake magana a kai da jama’a musamman ‘ya’yan jam’iyyar PDP na jihar Kebbi aka nada Janar Ishaya Bamaiyi a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a jihar Kebbi.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

“Muna so mu bayyana cewa nadin ya wanzu ne kawai a cikin tunanin Kabiru Tanimu Tukari, SAN, amma ba da yawun Jam’iyyar a matakin jiha ko a Tarayya ba.”

Ya ce hakika an kafa kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa a jihar Kebbi kamar yadda shugabannin jam’iyyar na kasa suka bayar a wata daya da ya gabata, inda ya kara da cewa majalisar yakin neman zaben shugaban kasa tana karkashin jagorancin Dakta Bello Haliru, wanda shi ne tsohon shugaban Jam’iyyar PDP na kasa.

Shugaban ya ce bin umarnin hedkwatar kasa, “Duk jihar da ba jam’iyya ba ce, babban jigo a jam’iyyar ya zama shugaban kwamitin yakin neman zabe, yayin da mai rike da tuta na gwamna ya zama mataimakinsa, don haka Dakta Bello Haliru da Janar Aminu Bande mai ritaya su ne ke rike da Jagorancin shugabancin yakin neman zaben Shugaban kasa a Jihar.”

A cewarsa, Darakta Janar din jam’iyyar guda daya ne kawai, majalisar yakin neman zaben shugaban kasa, wanda shi ne Gwamna Aminu Tambuwal na Jihar Sakkwato, yayin da Jihohi ke da shugabanni ba Darakta Janar ba .

Daga karshe Alhaji Usman Bello-Suru ya yi kira ga jama’a da su yi watsi da labaran da aka wallafa a kafafen yada labarai, yana mai jaddada cewa PDP na nan daram a Jihar Kebbi domin kuwa Kabiru Tanimu-Turaki bai wakiltan kowa dangane da shugabanci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidajen Man Da Ke Boye Mai A Yobe

Next Post

Za A Yi Wa ‘Ƴan Siyasa Da Ma’aikatan Shari’a Ƙarin Albashi A Nijeriya

Related

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

6 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Siyasa

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

1 day ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

3 days ago
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

3 days ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

3 days ago
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
Da ɗumi-ɗuminsa

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

4 days ago
Next Post
Buhari Zai Gabatar Da Kasafin Kudi Na N19.76tn Na 2023 A Majalisar Wakilai Ranar Juma’a

Za A Yi Wa 'Ƴan Siyasa Da Ma'aikatan Shari'a Ƙarin Albashi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.