ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ba Mu Nada Janar Bamaiyi A Matsayin Daraktan Yakin Zaben PDP A Kebbi Ba – Jam’iyyar

by Sulaiman and Umar Faruk
4 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP a jihar Kebbi ta musanta nada Janar Ishaya Bamaiyi a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa Atiku Abubakar a yayin babban zaben 2023 da ke tafe.

Shugaban jam’iyyar a jihar, Alhaji Usman Bello-Suru, shi ne ya bayyana haka a Birnin Kebbi, babban birnin jihar yayin da yake mayar da martani ga wani rahoton yanar gizo da daya daga cikin jaridun nan kasa (Wacce ba namu ba) ta wallafa.

  • Jam’iyyar PDP A Kebbi Ta Shirya Tarbar Dan Takarar Shugaban Kasa, Atiku Abubakar

Wakilinmu LEADERSHIP ya ruwaito wannan labarin ya fito ne daga wani taron manema labarai da Alhaji Kabiru Tanimu-Turaki, Shugaban kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP (BOT) kuma tsohon ministan ayyuka na musamman ne ya bayar a baya.

ADVERTISEMENT

Alhaji Bello-Suru ya ce: “Hankalin jam’iyyar PDP a jihar Kebbi ya karkata ne ga wata hira da aka wallafa da Alhaji Kabiru Tanimu Turaki (SAN) ya yi da manema labarai kuma jaridar ta buga a dandalinta na yanar gizo mai taken: “PDP ta nada Janar Bamaiyi Darakta Janar na yakin neman zaben Atiku Abubakar a shugaban kasa na Jihar Kebbi”.

“Tattaunawar da aka yi a kafafen yada labarai da ake magana a kai da jama’a musamman ‘ya’yan jam’iyyar PDP na jihar Kebbi aka nada Janar Ishaya Bamaiyi a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a jihar Kebbi.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Muna so mu bayyana cewa nadin ya wanzu ne kawai a cikin tunanin Kabiru Tanimu Tukari, SAN, amma ba da yawun Jam’iyyar a matakin jiha ko a Tarayya ba.”

Ya ce hakika an kafa kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa a jihar Kebbi kamar yadda shugabannin jam’iyyar na kasa suka bayar a wata daya da ya gabata, inda ya kara da cewa majalisar yakin neman zaben shugaban kasa tana karkashin jagorancin Dakta Bello Haliru, wanda shi ne tsohon shugaban Jam’iyyar PDP na kasa.

Shugaban ya ce bin umarnin hedkwatar kasa, “Duk jihar da ba jam’iyya ba ce, babban jigo a jam’iyyar ya zama shugaban kwamitin yakin neman zabe, yayin da mai rike da tuta na gwamna ya zama mataimakinsa, don haka Dakta Bello Haliru da Janar Aminu Bande mai ritaya su ne ke rike da Jagorancin shugabancin yakin neman zaben Shugaban kasa a Jihar.”

A cewarsa, Darakta Janar din jam’iyyar guda daya ne kawai, majalisar yakin neman zaben shugaban kasa, wanda shi ne Gwamna Aminu Tambuwal na Jihar Sakkwato, yayin da Jihohi ke da shugabanni ba Darakta Janar ba .

Daga karshe Alhaji Usman Bello-Suru ya yi kira ga jama’a da su yi watsi da labaran da aka wallafa a kafafen yada labarai, yana mai jaddada cewa PDP na nan daram a Jihar Kebbi domin kuwa Kabiru Tanimu-Turaki bai wakiltan kowa dangane da shugabanci.

PDP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
PDP
Umar Faruk
+ posts Bio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Buhari Zai Gabatar Da Kasafin Kudi Na N19.76tn Na 2023 A Majalisar Wakilai Ranar Juma’a

Za A Yi Wa 'Ƴan Siyasa Da Ma'aikatan Shari'a Ƙarin Albashi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.