• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Buhari

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bukaci Jami’an Tsaron Nijeriya da su zama ‘yan ba ruwan mu, su kauracewa shiga harkokin siyasa tare da ci-gaba da aiki a bisa ga kundin tsarin mulkin Nijeriya domin tabbatar da nasarar Babban Zaben 2023.

Da yake bude Babban Taron Shugaban Rundunar Soji na 2022 yau a Sakkwato, Buhari ya yi kira ga jami’an soji da su ci-gaba da mutunta ‘yancin dan -Adam a yayin kai farmaki a karkashin tsarin da duniya ta aminta da shi.

  • EFCC Ta Ayyana Neman Dan Takarar Sanatan APC A Kano, A.A Zaura Ruwa-a-jallo

Shugaban ya yi alkawalin ci-gaba da kokarin kara zamanantar da Rundunar Tsaro ciki har da inganta fannin sha’anin jiragen sama na jami’an sojin Kasa.

Buhari

A kan sha’anin Babban Zaben 2023, Shugaba Buhari ya bayyana cewar jami’an soji da Rundunar Tsaro bakidaya suna mutunta farar hula ta hanyar bayar da ingantaccen yanayin gudanar da zabe lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

Ya nuna jin dadinsa kan yadda Shugaban Rundunar Soji ya gabatar da bitar ka’idoji da dokokin da sojoji za su yi aiki da su a yayin zaben 2023 yana cewar akwai bukatar sojojin su maimaita kwarewar da suka nuna a zabukan Jihohin Anambra, Ekiti da Osun.

Buhari

A kan Babban Taron sojojin na bana kan bitar nasarorin da kalubalen da aka samu a 2022 da shirin tunkarar 2023, Buhari ya kalubalanci sojojin da su himmatu wajen bitar nasarorin da aka samu su kuma tabbatar da dorewar su domin bunkasa tsaro a fadin Kasa.

A jawabinsa Shugaban Rundunar Sojojin Kasa, Laftanar – Janar Faruk Yahaya ya bayyana cewar Sojojin Nijeriya sun samu gagarumar nasarar kawar da ta’addanci da shawo kan matsalolin tsaro a sassan Kasar nan bakidaya.

Ya ce daga Arewa- Maso- Gabas zuwa Arewa- Maso Yamma, zuwa Kudu- Maso Gabas da Kudu- Maso- Yamma duka sun taka muhimmiyar rawar ganin tabbatar da tsaro a fadin Kasa tare da taimakon makwabtan Kasashe ta hanyar hanawa ‘yan ta’adda cin karensu ba babbaka.

Shugaban Sojojin ya kara da cewar dimbin manyan makamai, bindigogi da harsasai da suka samu nasarar kwatowa a hannun ‘yan ta’adda ya karawa Rundunar Sojojin Nijeriya kwarin guiwa sosai.

Buhari

Ya kuma ce sun bayar da muhimmanci sosai ga kula da walwala da jin dadin sojoji, fitowa da tsarin ba da bashi da dama tare da gyaran barikin sojoji domin inganta jin dadin su.

A jawabinsa mai masaukin baki, Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Jihar Sakkwato ya godewa Buhari kan halartar taron tare da yabawa kokarin da Rundunar Soja da dukkanin Shugabannin Hukumomin Tsaro ke yi wajen tabbatar da ingantaccen tsaro a Sakkwato da Arewa Maso-Yamma bakidaya.

Ya ce Gwamnatinsa ta na bayar da dukkanin gudunmuwa da cikakken goyon baya ga jami’an tsaro a fadin Jihar. Ya ce Gwamnatinsa ta kara adadin alawus din da take baiwa jami’an tsaro zuwa kashi 150% domin kara masu kwarin guiwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Next Post
Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu ‘Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu 'Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.