• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bukaci Jami’an Tsaron Nijeriya da su zama ‘yan ba ruwan mu, su kauracewa shiga harkokin siyasa tare da ci-gaba da aiki a bisa ga kundin tsarin mulkin Nijeriya domin tabbatar da nasarar Babban Zaben 2023.

Da yake bude Babban Taron Shugaban Rundunar Soji na 2022 yau a Sakkwato, Buhari ya yi kira ga jami’an soji da su ci-gaba da mutunta ‘yancin dan -Adam a yayin kai farmaki a karkashin tsarin da duniya ta aminta da shi.

  • EFCC Ta Ayyana Neman Dan Takarar Sanatan APC A Kano, A.A Zaura Ruwa-a-jallo

Shugaban ya yi alkawalin ci-gaba da kokarin kara zamanantar da Rundunar Tsaro ciki har da inganta fannin sha’anin jiragen sama na jami’an sojin Kasa.

Buhari

A kan sha’anin Babban Zaben 2023, Shugaba Buhari ya bayyana cewar jami’an soji da Rundunar Tsaro bakidaya suna mutunta farar hula ta hanyar bayar da ingantaccen yanayin gudanar da zabe lafiya.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A FaÉ—in Nijeriya

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

Ya nuna jin dadinsa kan yadda Shugaban Rundunar Soji ya gabatar da bitar ka’idoji da dokokin da sojoji za su yi aiki da su a yayin zaben 2023 yana cewar akwai bukatar sojojin su maimaita kwarewar da suka nuna a zabukan Jihohin Anambra, Ekiti da Osun.

Buhari

A kan Babban Taron sojojin na bana kan bitar nasarorin da kalubalen da aka samu a 2022 da shirin tunkarar 2023, Buhari ya kalubalanci sojojin da su himmatu wajen bitar nasarorin da aka samu su kuma tabbatar da dorewar su domin bunkasa tsaro a fadin Kasa.

A jawabinsa Shugaban Rundunar Sojojin Kasa, Laftanar – Janar Faruk Yahaya ya bayyana cewar Sojojin Nijeriya sun samu gagarumar nasarar kawar da ta’addanci da shawo kan matsalolin tsaro a sassan Kasar nan bakidaya.

Ya ce daga Arewa- Maso- Gabas zuwa Arewa- Maso Yamma, zuwa Kudu- Maso Gabas da Kudu- Maso- Yamma duka sun taka muhimmiyar rawar ganin tabbatar da tsaro a fadin Kasa tare da taimakon makwabtan Kasashe ta hanyar hanawa ‘yan ta’adda cin karensu ba babbaka.

Shugaban Sojojin ya kara da cewar dimbin manyan makamai, bindigogi da harsasai da suka samu nasarar kwatowa a hannun ‘yan ta’adda ya karawa Rundunar Sojojin Nijeriya kwarin guiwa sosai.

Buhari

Ya kuma ce sun bayar da muhimmanci sosai ga kula da walwala da jin dadin sojoji, fitowa da tsarin ba da bashi da dama tare da gyaran barikin sojoji domin inganta jin dadin su.

A jawabinsa mai masaukin baki, Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Jihar Sakkwato ya godewa Buhari kan halartar taron tare da yabawa kokarin da Rundunar Soja da dukkanin Shugabannin Hukumomin Tsaro ke yi wajen tabbatar da ingantaccen tsaro a Sakkwato da Arewa Maso-Yamma bakidaya.

Ya ce Gwamnatinsa ta na bayar da dukkanin gudunmuwa da cikakken goyon baya ga jami’an tsaro a fadin Jihar. Ya ce Gwamnatinsa ta kara adadin alawus din da take baiwa jami’an tsaro zuwa kashi 150% domin kara masu kwarin guiwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sahihanci Shi Ne Tushen Hadin Gwiwar Afirka Da Sin

Next Post

Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu ‘Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

Related

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A FaÉ—in Nijeriya
Da É—umi-É—uminsa

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A FaÉ—in Nijeriya

57 minutes ago
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

1 hour ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

2 hours ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

3 hours ago
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar HaÉ—aka Ta ADC
Labarai

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar HaÉ—aka Ta ADC

12 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da É—umi-É—uminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

13 hours ago
Next Post
Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu ‘Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu 'Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A FaÉ—in Nijeriya

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A FaÉ—in Nijeriya

July 8, 2025
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

July 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da ÆŠumi-ÆŠumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da ÆŠumi-ÆŠumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar HaÉ—aka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar HaÉ—aka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.