ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
4 years ago
Buhari

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bukaci Jami’an Tsaron Nijeriya da su zama ‘yan ba ruwan mu, su kauracewa shiga harkokin siyasa tare da ci-gaba da aiki a bisa ga kundin tsarin mulkin Nijeriya domin tabbatar da nasarar Babban Zaben 2023.

Da yake bude Babban Taron Shugaban Rundunar Soji na 2022 yau a Sakkwato, Buhari ya yi kira ga jami’an soji da su ci-gaba da mutunta ‘yancin dan -Adam a yayin kai farmaki a karkashin tsarin da duniya ta aminta da shi.

  • EFCC Ta Ayyana Neman Dan Takarar Sanatan APC A Kano, A.A Zaura Ruwa-a-jallo

Shugaban ya yi alkawalin ci-gaba da kokarin kara zamanantar da Rundunar Tsaro ciki har da inganta fannin sha’anin jiragen sama na jami’an sojin Kasa.

ADVERTISEMENT

Buhari

A kan sha’anin Babban Zaben 2023, Shugaba Buhari ya bayyana cewar jami’an soji da Rundunar Tsaro bakidaya suna mutunta farar hula ta hanyar bayar da ingantaccen yanayin gudanar da zabe lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ya nuna jin dadinsa kan yadda Shugaban Rundunar Soji ya gabatar da bitar ka’idoji da dokokin da sojoji za su yi aiki da su a yayin zaben 2023 yana cewar akwai bukatar sojojin su maimaita kwarewar da suka nuna a zabukan Jihohin Anambra, Ekiti da Osun.

Buhari

A kan Babban Taron sojojin na bana kan bitar nasarorin da kalubalen da aka samu a 2022 da shirin tunkarar 2023, Buhari ya kalubalanci sojojin da su himmatu wajen bitar nasarorin da aka samu su kuma tabbatar da dorewar su domin bunkasa tsaro a fadin Kasa.

A jawabinsa Shugaban Rundunar Sojojin Kasa, Laftanar – Janar Faruk Yahaya ya bayyana cewar Sojojin Nijeriya sun samu gagarumar nasarar kawar da ta’addanci da shawo kan matsalolin tsaro a sassan Kasar nan bakidaya.

Ya ce daga Arewa- Maso- Gabas zuwa Arewa- Maso Yamma, zuwa Kudu- Maso Gabas da Kudu- Maso- Yamma duka sun taka muhimmiyar rawar ganin tabbatar da tsaro a fadin Kasa tare da taimakon makwabtan Kasashe ta hanyar hanawa ‘yan ta’adda cin karensu ba babbaka.

Shugaban Sojojin ya kara da cewar dimbin manyan makamai, bindigogi da harsasai da suka samu nasarar kwatowa a hannun ‘yan ta’adda ya karawa Rundunar Sojojin Nijeriya kwarin guiwa sosai.

Buhari

Ya kuma ce sun bayar da muhimmanci sosai ga kula da walwala da jin dadin sojoji, fitowa da tsarin ba da bashi da dama tare da gyaran barikin sojoji domin inganta jin dadin su.

A jawabinsa mai masaukin baki, Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Jihar Sakkwato ya godewa Buhari kan halartar taron tare da yabawa kokarin da Rundunar Soja da dukkanin Shugabannin Hukumomin Tsaro ke yi wajen tabbatar da ingantaccen tsaro a Sakkwato da Arewa Maso-Yamma bakidaya.

Ya ce Gwamnatinsa ta na bayar da dukkanin gudunmuwa da cikakken goyon baya ga jami’an tsaro a fadin Jihar. Ya ce Gwamnatinsa ta kara adadin alawus din da take baiwa jami’an tsaro zuwa kashi 150% domin kara masu kwarin guiwa.

Buhari
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Siyasar 2027: Yadda Ƴan Adawa Ke Ƙara Shiga Tsaka-mai-wuya

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu ‘Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu 'Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.