ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Buhari Ya Hori Jami’an Tsaro Su Zama ‘Yan Ba Ruwanmu A Siyasa

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
4 years ago
Buhari

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bukaci Jami’an Tsaron Nijeriya da su zama ‘yan ba ruwan mu, su kauracewa shiga harkokin siyasa tare da ci-gaba da aiki a bisa ga kundin tsarin mulkin Nijeriya domin tabbatar da nasarar Babban Zaben 2023.

Da yake bude Babban Taron Shugaban Rundunar Soji na 2022 yau a Sakkwato, Buhari ya yi kira ga jami’an soji da su ci-gaba da mutunta ‘yancin dan -Adam a yayin kai farmaki a karkashin tsarin da duniya ta aminta da shi.

  • EFCC Ta Ayyana Neman Dan Takarar Sanatan APC A Kano, A.A Zaura Ruwa-a-jallo

Shugaban ya yi alkawalin ci-gaba da kokarin kara zamanantar da Rundunar Tsaro ciki har da inganta fannin sha’anin jiragen sama na jami’an sojin Kasa.

ADVERTISEMENT

Buhari

A kan sha’anin Babban Zaben 2023, Shugaba Buhari ya bayyana cewar jami’an soji da Rundunar Tsaro bakidaya suna mutunta farar hula ta hanyar bayar da ingantaccen yanayin gudanar da zabe lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ya nuna jin dadinsa kan yadda Shugaban Rundunar Soji ya gabatar da bitar ka’idoji da dokokin da sojoji za su yi aiki da su a yayin zaben 2023 yana cewar akwai bukatar sojojin su maimaita kwarewar da suka nuna a zabukan Jihohin Anambra, Ekiti da Osun.

Buhari

A kan Babban Taron sojojin na bana kan bitar nasarorin da kalubalen da aka samu a 2022 da shirin tunkarar 2023, Buhari ya kalubalanci sojojin da su himmatu wajen bitar nasarorin da aka samu su kuma tabbatar da dorewar su domin bunkasa tsaro a fadin Kasa.

A jawabinsa Shugaban Rundunar Sojojin Kasa, Laftanar – Janar Faruk Yahaya ya bayyana cewar Sojojin Nijeriya sun samu gagarumar nasarar kawar da ta’addanci da shawo kan matsalolin tsaro a sassan Kasar nan bakidaya.

Ya ce daga Arewa- Maso- Gabas zuwa Arewa- Maso Yamma, zuwa Kudu- Maso Gabas da Kudu- Maso- Yamma duka sun taka muhimmiyar rawar ganin tabbatar da tsaro a fadin Kasa tare da taimakon makwabtan Kasashe ta hanyar hanawa ‘yan ta’adda cin karensu ba babbaka.

Shugaban Sojojin ya kara da cewar dimbin manyan makamai, bindigogi da harsasai da suka samu nasarar kwatowa a hannun ‘yan ta’adda ya karawa Rundunar Sojojin Nijeriya kwarin guiwa sosai.

Buhari

Ya kuma ce sun bayar da muhimmanci sosai ga kula da walwala da jin dadin sojoji, fitowa da tsarin ba da bashi da dama tare da gyaran barikin sojoji domin inganta jin dadin su.

A jawabinsa mai masaukin baki, Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Jihar Sakkwato ya godewa Buhari kan halartar taron tare da yabawa kokarin da Rundunar Soja da dukkanin Shugabannin Hukumomin Tsaro ke yi wajen tabbatar da ingantaccen tsaro a Sakkwato da Arewa Maso-Yamma bakidaya.

Ya ce Gwamnatinsa ta na bayar da dukkanin gudunmuwa da cikakken goyon baya ga jami’an tsaro a fadin Jihar. Ya ce Gwamnatinsa ta kara adadin alawus din da take baiwa jami’an tsaro zuwa kashi 150% domin kara masu kwarin guiwa.

Buhari
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Shekara 200 Bayan Shehu Ɗan Fodiyo: Hubbarensa Na Ci Gaba Zama Wajen Ziyara Da Neman Tabarruki
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu ‘Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

Tura Mu Aka Yi Mu Sace Sanatan APC- Wasu 'Yan Bindiga Da Suka Shiga Hannu

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.