• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Matukar Mutum Ba Shi Da Katin Zabe Ba Zai Jefa Kuri’a Ba – INEC

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
2023: Matukar Mutum Ba Shi Da Katin Zabe Ba Zai Jefa Kuri’a Ba – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta shawarci duk wanda ya san ya yi rajistar zaɓe, to ya gaggauta zuwa karɓar katin shaidar rajistar sa PVC, domin babu wanda za a bari ya yi zaɓen 2023 ba tare da katin rajista ba.

 

Kwamishinan INEC na Jihar Katsina, Farfesa Ibrahim Yahaya Maƙarfi, shi ne ya jaddada haka a cikin wata tattaunawa da ya yi da manema labarai a ranar Lahadi a Katsina.

  • 2023: INEC Ta Gargadi Masu Sayar Da Katin Zabensu Ga ‘Yan Siyasa

Ya ce hukumar ba za ta bai wa wani uzirin yin zaɓe ba tare da katin shaidar rajista ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Ya ce INEC ta dakatar da ci gaba da rajistar masu zaɓe tun a ranar 31 ga Yuli, saboda tilas sai an ɗauki lokaci ana tattarawa, tantancewa da kuma taskace sunaye da bayanan waɗanda aka yi wa rajistar, kafin a kai ga buga wa kowa katin rajista.

 

Maƙarfi ya ce ta wannan tsarin ne INEC ke wa masu zaɓe rajistar da za ta ba su damar zaɓen duk wani ko wata ‘yan takarar da su ke so su zaɓa.

 

Ya ce: “Sashe na 16(1) na Dokar Zaɓe ya wajibta wa INEC yi wa masu zaɓe rajista, buga katin rajista da kuma damƙa wa duk wanda ya yi rajista katin sa a hannu. Amma tilas sai wanda sunan sa ya fito a jerin sunayen da ke cikin rajista kaɗai za a iya bai wa katin zaɓe.

 

“Ya na da kyau a san cewa katin shaidar rajista shi ne shaidar amincewa mutum ya yi zaɓe, kamar yada Sashe na 47 na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar.

 

“Daga ranar 12 ga Disamba INEC za ta fara raba katin shaidar rajistar zaɓe, har zuwa ranar 22 ga Janairu, 2023.

 

“Za mu raba katin a dukkan ƙananan hukumomi 34 na jiha, kuma za a koma ana rabawa a dukkan cibiyoyin rajistar zaɓe 361 na jiha daga ranar 6 zuwa 15 ga Janairu, 2023.”

 

INEC ta yi kira ga duk wanda ya san ya yi rajista ya je ya karɓi katin sa. Hukumar ta ƙara yin sanarwar cewa za a riƙa raba katin tun daga ƙarfe 9 na safe har zuwa 3 na yamma, a kullum har da ranakun Asabar da Lahadi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kafa Dokar Hana Shan Sigari A New Zealand

Next Post

Yadda Dangin Ango Da Amarya Suka Bai Wa Hammata Iska Kan Sadaki 

Related

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

38 minutes ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

4 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

6 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

20 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

20 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

21 hours ago
Next Post
Yadda Dangin Ango Da Amarya Suka Bai Wa Hammata Iska Kan Sadaki 

Yadda Dangin Ango Da Amarya Suka Bai Wa Hammata Iska Kan Sadaki 

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.