ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Matukar Mutum Ba Shi Da Katin Zabe Ba Zai Jefa Kuri’a Ba – INEC

by Sulaiman
4 years ago
Katin Zabe

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta shawarci duk wanda ya san ya yi rajistar zaɓe, to ya gaggauta zuwa karɓar katin shaidar rajistar sa PVC, domin babu wanda za a bari ya yi zaɓen 2023 ba tare da katin rajista ba.

 

Kwamishinan INEC na Jihar Katsina, Farfesa Ibrahim Yahaya Maƙarfi, shi ne ya jaddada haka a cikin wata tattaunawa da ya yi da manema labarai a ranar Lahadi a Katsina.

ADVERTISEMENT
  • 2023: INEC Ta Gargadi Masu Sayar Da Katin Zabensu Ga ‘Yan Siyasa

Ya ce hukumar ba za ta bai wa wani uzirin yin zaɓe ba tare da katin shaidar rajista ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ya ce INEC ta dakatar da ci gaba da rajistar masu zaɓe tun a ranar 31 ga Yuli, saboda tilas sai an ɗauki lokaci ana tattarawa, tantancewa da kuma taskace sunaye da bayanan waɗanda aka yi wa rajistar, kafin a kai ga buga wa kowa katin rajista.

 

Maƙarfi ya ce ta wannan tsarin ne INEC ke wa masu zaɓe rajistar da za ta ba su damar zaɓen duk wani ko wata ‘yan takarar da su ke so su zaɓa.

 

Ya ce: “Sashe na 16(1) na Dokar Zaɓe ya wajibta wa INEC yi wa masu zaɓe rajista, buga katin rajista da kuma damƙa wa duk wanda ya yi rajista katin sa a hannu. Amma tilas sai wanda sunan sa ya fito a jerin sunayen da ke cikin rajista kaɗai za a iya bai wa katin zaɓe.

 

“Ya na da kyau a san cewa katin shaidar rajista shi ne shaidar amincewa mutum ya yi zaɓe, kamar yada Sashe na 47 na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar.

 

“Daga ranar 12 ga Disamba INEC za ta fara raba katin shaidar rajistar zaɓe, har zuwa ranar 22 ga Janairu, 2023.

 

“Za mu raba katin a dukkan ƙananan hukumomi 34 na jiha, kuma za a koma ana rabawa a dukkan cibiyoyin rajistar zaɓe 361 na jiha daga ranar 6 zuwa 15 ga Janairu, 2023.”

 

INEC ta yi kira ga duk wanda ya san ya yi rajista ya je ya karɓi katin sa. Hukumar ta ƙara yin sanarwar cewa za a riƙa raba katin tun daga ƙarfe 9 na safe har zuwa 3 na yamma, a kullum har da ranakun Asabar da Lahadi.

Katin Zabe
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Yadda Dangin Ango Da Amarya Suka Bai Wa Hammata Iska Kan Sadaki 

Yadda Dangin Ango Da Amarya Suka Bai Wa Hammata Iska Kan Sadaki 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.