• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanatoci guda uku dukkaninsu ‘ya’yan Jam’iuyar APC ne masu ci a halin yanzu daga jihar Bauchi kuma dukkaninsu babu wanda zai sake komawa Majalisar Dattawa ta kasa daga bayan zaben 2023 domin kuwa sun sha kaye a zaben fitar da gwani da jam’iyyar APC ta gudanar a jihar na Bauchi.

Bayanan da wakilinmu ya tattaro daga jihar ta Bauchi ya nuna cewa Sanatoci guda biyu Lawan Yahaya Gumau (Sanatan Bauchi ta Kudu) da Sanata Adamu Bulkachuwa (Sanatan Bauchi ta Arewa) sun fito neman a sake zabensu a wannan kujerun nasu, inda daliget suka yi waje da su ta hanyar kin zabarsu. Yayin da kuma Sanata Halluru Dauda Jika (Sanatan Bauchi ta tsakiya) ya fito neman tikitin gwamna a jam’iyyar APC wanda kuma ya sha kaye.

  • 2023: Jm’iyyar APC Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya

A zaben da aka gudanar na neman tikitin kujerar Sanata a karkashin jam’iyyar APC, wakilinmu ya labarto mana cewa Hon. Sirajo Ibrahim Tanko ne ya samu gagarumar nasarar lashe zaben tikitin Sanatan Bauchi ta Arewa inda ya kada Sanatan da ke ci a halin yanzu Sanata Adamu Bulkachuwa da mummunan rinjaye saboda daliget sunma ki jefa masa kuri’a gaba daya.

Sannan a zaben kujerar Sanatan Bauchi ta Kudu, Hon. Shehu Buba shi ne ya kada Sanatan mai ci, Lawan Yahaya Gumau da kuri’u kalilan.

Sai kuma tikitin Sanatan Bauchi ta tsakiya wanda tsohon shugaban jam’iyyar APC reshen jihar Bauchi, Alhaji Uba Ahmad Nana, ya samu nasarar kada abokan takararsa da suka hada da Sanata Isa Hamma Misau da Hon. Abubakar Shehu.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

Kazalika, Sanatan da ke ci a wannan kujerar ta Bauchi ta tsakiya a halin yanzu, Sanata Halliru Dauda Jika, bai fito takarar Sanatan ba domin ya fito an dama da shi ne wajen neman tikitin APC a kujerar gwamnan Jihar Bauchi wanda kuma ya sha kasa a hannun, Air Marshal Sadiq Baba Abubakar.

Tunin Jam’iyyu suka ja daga na neman nasara a kujerun Sanatan musamman jam’iyyar APC da PDP domin dukkaninsu sun yi zaben cikin gida na sanatoci da za su rike musu tuta a zaben 2023.

Da wannan matakin al’umar jihar Bauchi ke sa ran yin sabbin sanatoci daga Jam’iyyun da za su samu nasara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Jm’iyyar APC Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya

Next Post

‘Yan Nijeriya Mu Hankalta, Wasan Kwaikwayo ‘Yan Siyasa Ke Yi Da Mu, In Ji Matasan Arewa A Kudu

Related

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

2 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

4 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

6 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

7 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

1 week ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya GargaÉ—i Magoya Bayan Wike A PDP

1 week ago
Next Post
Yan Nijeriya

‘Yan Nijeriya Mu Hankalta, Wasan Kwaikwayo ‘Yan Siyasa Ke Yi Da Mu, In Ji Matasan Arewa A Kudu

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.