• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanatoci guda uku dukkaninsu ‘ya’yan Jam’iuyar APC ne masu ci a halin yanzu daga jihar Bauchi kuma dukkaninsu babu wanda zai sake komawa Majalisar Dattawa ta kasa daga bayan zaben 2023 domin kuwa sun sha kaye a zaben fitar da gwani da jam’iyyar APC ta gudanar a jihar na Bauchi.

Bayanan da wakilinmu ya tattaro daga jihar ta Bauchi ya nuna cewa Sanatoci guda biyu Lawan Yahaya Gumau (Sanatan Bauchi ta Kudu) da Sanata Adamu Bulkachuwa (Sanatan Bauchi ta Arewa) sun fito neman a sake zabensu a wannan kujerun nasu, inda daliget suka yi waje da su ta hanyar kin zabarsu. Yayin da kuma Sanata Halluru Dauda Jika (Sanatan Bauchi ta tsakiya) ya fito neman tikitin gwamna a jam’iyyar APC wanda kuma ya sha kaye.

  • 2023: Jm’iyyar APC Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya

A zaben da aka gudanar na neman tikitin kujerar Sanata a karkashin jam’iyyar APC, wakilinmu ya labarto mana cewa Hon. Sirajo Ibrahim Tanko ne ya samu gagarumar nasarar lashe zaben tikitin Sanatan Bauchi ta Arewa inda ya kada Sanatan da ke ci a halin yanzu Sanata Adamu Bulkachuwa da mummunan rinjaye saboda daliget sunma ki jefa masa kuri’a gaba daya.

Sannan a zaben kujerar Sanatan Bauchi ta Kudu, Hon. Shehu Buba shi ne ya kada Sanatan mai ci, Lawan Yahaya Gumau da kuri’u kalilan.

Sai kuma tikitin Sanatan Bauchi ta tsakiya wanda tsohon shugaban jam’iyyar APC reshen jihar Bauchi, Alhaji Uba Ahmad Nana, ya samu nasarar kada abokan takararsa da suka hada da Sanata Isa Hamma Misau da Hon. Abubakar Shehu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Kazalika, Sanatan da ke ci a wannan kujerar ta Bauchi ta tsakiya a halin yanzu, Sanata Halliru Dauda Jika, bai fito takarar Sanatan ba domin ya fito an dama da shi ne wajen neman tikitin APC a kujerar gwamnan Jihar Bauchi wanda kuma ya sha kasa a hannun, Air Marshal Sadiq Baba Abubakar.

Tunin Jam’iyyu suka ja daga na neman nasara a kujerun Sanatan musamman jam’iyyar APC da PDP domin dukkaninsu sun yi zaben cikin gida na sanatoci da za su rike musu tuta a zaben 2023.

Da wannan matakin al’umar jihar Bauchi ke sa ran yin sabbin sanatoci daga Jam’iyyun da za su samu nasara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Jm’iyyar APC Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya

Next Post

‘Yan Nijeriya Mu Hankalta, Wasan Kwaikwayo ‘Yan Siyasa Ke Yi Da Mu, In Ji Matasan Arewa A Kudu

Related

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

2 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

3 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

4 days ago
Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai FaÉ—i – Shehu Sani
Manyan Labarai

Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai FaÉ—i – Shehu Sani

4 days ago
PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke
Siyasa

PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

5 days ago
Next Post
Yan Nijeriya

‘Yan Nijeriya Mu Hankalta, Wasan Kwaikwayo ‘Yan Siyasa Ke Yi Da Mu, In Ji Matasan Arewa A Kudu

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.