• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP, Atiku Abubakar, Wazirin Adamawa ya yi alƙawarin cewa zai mayar da hankalin sa wajen farfaɗo da harkokin ilmi tare da inganta shi, ya na mai zargin cewa, “gwamnatin APC ta kashe harkar ilmi a ƙasar nan, ta hanyar bijiro da tsare-tsaren da kowa ya san ba za su inganta ci gaban ilmi ba.”

Atiku ya bayyana haka ne a yayin ƙaddamar da fara kamfen ɗin sa na shiyyar Kudu maso Yamma a Akure, babban birnin Jihar Ondo cikin makon nan.

  • Mijina Wayayyen Bafulatani Ne, Ba Bafulatanin Daji Ba Ne – Uwargidan Atiku

Daga nan ya ƙara jaddada irin alƙawarin da ya yi a Ilorin, wanda ya ce idan ya yi nasara, gwamnatin sa za ta ware dala biliyan 10 domin bunƙasa ƙanana da matsakaitan masana’antu, ta yadda matasa za su yunƙuro wajen samun aikin yi sosai, su ma mata rayuwar su za ta ƙara bunƙasa.

Da ya ke jawabi a wurin gangamin, wanda ya samu halartar ɗimbin magoya bayan PDP, Atiku ya ce Nijeriya ta yi asarar shekaru takwas da APC ta yi ta na mulki, wanda su ka jefa jama’a cikin mawuyacin halin da ba shi misaltuwa.

Atiku

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Ya yi fatan cewa, “daga 2023, kada Allah ya sake jarabtar ‘yan Nijeriya da irin mulkin APC.”

Kafin ya fara jawabi, sai da uwargidan sa Titi Abubakar ta fara yi wa dandazon magoya bayan PDP jawabi tukunna.

Titi, wadda haifaffiyar Jihar Ondo ce, ta ce ta yi farin cikin ganin PDP ta fara kamfen ɗin shiyyar Kudu maso Yamma a jihar ta ta haihuwa.

“Ina gabatar da kai na a gare ku, a matsayi na na ‘yar ku. Idan ku ka zaɓi miji na, zai daƙile Boko Haram kuma zai inganta ilmi.

“Kada ku manta, miji na ne ya yi nasara a zaɓen 2019, amma aka yi masa maguɗi, aka murɗe zaɓen. To kada ku bari a sake yaudarar ku. Wannan lokacin ma ku fito ku sake zaɓen PDP.

“Idan Atiku ya yi nasara, wata dama ce da Jihar Ondo za ta samu cewa ‘yar su za ta zama uwargidan shugaban ƙasa. Dama kuma Bayarabiya ba ta taɓa zama uwargidan shugaban ƙasa a Najeriya ba.”

Atiku

Da ta ke yabon mijin ta, Titi ta ce ko lokacin da ya na mataimakin shugaban ƙasa ya yi rawar gani, domin shi ne ya janyo irin su Nasir El-Rufai da Ngozi Ikwenja-Ewela cikin gwamnati, “har da ma wasu fitattun haziƙan da su ka kawo ci gaba a ƙasar nan.

Mataimakin takarar Atiku, Gwamna Ifeanyi Okowa ya ce PDP za ta farfaɗo da fannin ilmi. Sannan ya nuna damuwar sa dangane da yadda ɗaliban jami’a su ka shafe watanni takwas a gida, ya na mai cewa ba za a samu irin haka a gwamnatin su ba.

Atiku

Shi ma Gwamna Udom Emmanuel ya roƙi al’ummar Jihar Ondo su zaɓi Atiku, wanda ya ce shi kaɗai a cikin sauran ‘yan takarar zai iya haɗa kan Najeriya.

Shugaban jam’iyya Iyorchia Ayu da Babban Daraktan Kamfen, wato Gwamna Aminu Tambuwal na Sokoto, duk sun yi wa taron jawabai masu nuna fifikon Atiku kan sauran ‘yan takara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Mai A Fadin Nijeriya – Dillalai

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

2 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

3 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

6 days ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Malta Guinness

Bikin Bukin Sallar Da Malta Guinness

June 5, 2025
Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.