• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ina Da Karfin Jiki, Lafiyayye Ne Ni, Tinubu Ya Warware Jita-jitar Rashin Lafiya A Bidiyo

by Muhammad
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Ina Da Karfin Jiki, Lafiyayye Ne Ni, Tinubu Ya Warware Jita-jitar Rashin Lafiya A Bidiyo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, daga can birnin Landan, ya shiga dandalin sada zumunta na yanar gizo ya wallafa wani bidiyonsa yana motsa jiki domin tabbatar da lafiyarsa.

A cikin wani gajeren faifan bidiyo da ya saka a daren Lahadi, an ga Tinubu akan keken motsa jiki, yana mai cewa sabanin rade-radin da ake yadawa, yana cikin koshin lafiya.

  • Tinubu: Jonathan Ba Zai Kubutar Da Kai A Zaben 2023 Ba —PDP
  • An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

Tinubu dai ya bar Nijeriya zuwa kasar Ingila, lamarin da ya haifar da cece-ku-ce a kan cewa tafiyar tasa ba za ta rasa nasaba da rashin lafiya mai tsanani ba, musamman ma a lokacin da ya fito fili a lokacin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da daukacin ‘yan takarar shugaban kasa da jam’iyyunsu suka yi.

Amma a cikin faifan bidiyon, wanda ya wallafa a shafin sa na Twitter da aka tabbatar, Tinubu ya kuma bar wani takaitaccen sako, yana mai cewa, “Da yawa sun ce na mutu; wasu kuma na cewa na janye daga yakin neman zaben shugaban kasa. To… a’a.

“Wannan ita ce gaskiya: Ina da ƙarfin jiki, ina cikin koshin lafiya kuma a shirye nake na bauta wa ‘yan Nijeriya tun daga ranar farko da na zama shugaban kasa.”

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Sakamakon rahotannin da ake zarginsa da rashin lafiyarsa, kungiyar yakin neman zaben jam’iyyar APC ta karyata jita-jitar, tare da nuna cewa Tinubu na cikin koshin lafiya.

Da yake mayar da martani ga wani hoton bogi da ya karade kafafen sada zumunta da ke nuna cewa Tinubu ba shi da lafiya, daraktan yada labarai da wayar da kan jama’a na kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bayo Onanuga, ya bayyana a shafinsa na Facebook cewa: “Ku kalli tagar gilashin sa. Bari in tabbatar wa ‘yan Nijeriya masu son sanin inda Tinubu yake. Yana Landan, a gidansa.

“Tinubu ya bar Nijeriya ne a daren ranar Asabar don hutu da kuma shirye-shiryen yakin neman zabe.

“Na gan shi na yi magana da shi sa’o’i biyu kafin ya tafi. Yana da hazaka da tausayi. lafiyarsa garau. Bai je jinyar wata cuta ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahaifiyar Shugaban KAROTA Baffa Babba DanAgundi Ta Rasu

Next Post

Ganduje Ya Jajantawa Shugaban KAROTA Baffa DanAgundi Sakamakon Rasuwar Mahaifiyarsa

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

1 day ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

1 day ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

3 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

4 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

6 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

7 days ago
Next Post
Ganduje Ya Jajantawa Shugaban KAROTA Baffa DanAgundi Sakamakon Rasuwar Mahaifiyarsa

Ganduje Ya Jajantawa Shugaban KAROTA Baffa DanAgundi Sakamakon Rasuwar Mahaifiyarsa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.