• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kungiyoyin Mata Da Matasa Sun Bukaci Sanata Jika Ya Koma NNPP Don Yin Takarar Gwamnan Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Kungiyoyin Mata Da Matasa Sun Bukaci Sanata Jika Ya Koma NNPP Don Yin Takarar Gwamnan Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu kungiyoyin mata da matasa a jihar Bauchi sun yi gangami a ofishin Sanata Halliru Dauda Jika inda suke kiransa da ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar NNPP mai alamar kwando da kayan marmari domin samun zarafin fitowa takarar gwamnan Jihar Bauchi a 2023 da ke tafe.

Wakilinmu ya labarto cewa Sanata Halliru Dauda Jika dai shine ke wakiltar mazabar Bauchi ta tsakiya a Majalisar Dattawa ya fito neman tikitin APC na kujerar gwamna amma Air Marshal Saddique Baba Abubakar ya kayar da shi a zaben fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar a kwanakin baya.

  • Dubban Jama’a Sun Shiga Jam’iyyar NNPP A Neja

Da ya ke jawabi a wajen gangamin, Sadik Abdullahi Kobi, Shugaban kungiyar mata masu dogaro da kansu na jihar Bauchi, ya shaida cewar, babban burinsu shine Sanatan ya amince ya fito neman takarar gwamna a karkashin jam’iyyar NNPP domin cire musu kitse a wuta.

Mata

Ya ce: “Wannan dandanzon mata da matasa da ka gani sun fito ne domin yin kira ga Sanata Halliru Dauda Jika da ya fice daga jam’iyyar APC ya shiga jam’iyyar NNPP domin ya samu damar yin takarar gwamnan Jihar Bauchi a 2023.”

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

“Daman mun gargadi uwar jam’iyyar APC ta dauki tikitin neman takarar gwamna ta bai wa Sanata Jika saboda shi ne yake tare da mutane, shi ne yake mutunta mutane, shine ya san matsalolinsu, shine yake kawo cigaba ga kuma shine suke so, sabanin wanda aka zo aka kakaba mana da karfin tsiya. Don haka muke son ya bar jam’iyyar ya koma NNPP mu kuma muna tare da shi dari bisa dari.

“Don haka mu a matsayinmu na mata da matasa muna nuna wa Sanata Jika hanyar da ya dace na cewa ya zo ya bi abun da jama’a ke so. Abun da jama’a ke so kuma shine ya shiga NNPP ya mana takarar gwamna.”

Mata

Abdullahi Kobi ya bada tabbacin cewa muddin Jika ya amince ya fito neman takarar gwamna a NNPP tabbas jama’an jihar za su zabeshi domin sun amince da salon jagorancinsa da kyautata musu, “al’umma ke kawo mutum musamman mata. Ka ga kuwa al’ummar ne suka ce lallai ya zo ya musu takara. Don haka muna da kyakkyawar fatan shine zai yi nasara a babban zaben 2023.”

A bangarenta, Malama Saliha Abubakar ta bayyana cewar a shirye suke su shiga lungu da sako domin nema wa Sanata Jika kuri’u, tana mai cewa sun amince da cewa ya fi kowani dan takara dacewar da zai iya jagorantar jihar Bauchi yadda ya kamata.

“Mu iyaye mata mune mu kan irin halin da muke cikin a hali yanzu. Don haka muna rokon ya amsa kiran mu ya koma NNPP domin mu mara masa baya.”

Da ya ke amsar bukatun kungiyoyin a madadin Sanatan, Haruna Muhammad daya daga cikin hadiman Sanata Jika, ya gode wa kungiyoyin bisa nuna damuwa da soyayya ga Sanata Halliru Dauda Jika ya kuma ba su tabbacin cewa za su yi zama na musamman kan wannan bukatar tare da daukan matakin da ya dace domin cigaban jihar Bauchi.

Ya ce, tabbas Sanata Jika na yi ne don al’umma kuma zai sauraro bukatunsu tare da yin abun da dace. Ya ba su tabbacin cewa da izinin Allah Sanata Jika zai yi takarar gwamna a 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Yarima Ne Kadai Zai Iya Dorawa Da Irin Nasarar Da Buhari Ya Samu A Mulki —Olumide

Next Post

Ku Ci Gaba Da Yada Labaran Cin Zarafin Mata Da Kananan Yara —CITAD

Related

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

1 day ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

2 days ago
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027
Siyasa

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

3 days ago
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027
Siyasa

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

4 days ago
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10
Siyasa

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

4 days ago
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
Siyasa

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

5 days ago
Next Post
Ku Ci Gaba Da Yada Labaran Cin Zarafin Mata Da Kananan Yara —CITAD

Ku Ci Gaba Da Yada Labaran Cin Zarafin Mata Da Kananan Yara —CITAD

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.