ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kungiyoyin Mata Da Matasa Sun Bukaci Sanata Jika Ya Koma NNPP Don Yin Takarar Gwamnan Bauchi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Mata

Wasu kungiyoyin mata da matasa a jihar Bauchi sun yi gangami a ofishin Sanata Halliru Dauda Jika inda suke kiransa da ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar NNPP mai alamar kwando da kayan marmari domin samun zarafin fitowa takarar gwamnan Jihar Bauchi a 2023 da ke tafe.

Wakilinmu ya labarto cewa Sanata Halliru Dauda Jika dai shine ke wakiltar mazabar Bauchi ta tsakiya a Majalisar Dattawa ya fito neman tikitin APC na kujerar gwamna amma Air Marshal Saddique Baba Abubakar ya kayar da shi a zaben fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar a kwanakin baya.

  • Dubban Jama’a Sun Shiga Jam’iyyar NNPP A Neja

Da ya ke jawabi a wajen gangamin, Sadik Abdullahi Kobi, Shugaban kungiyar mata masu dogaro da kansu na jihar Bauchi, ya shaida cewar, babban burinsu shine Sanatan ya amince ya fito neman takarar gwamna a karkashin jam’iyyar NNPP domin cire musu kitse a wuta.

ADVERTISEMENT

Mata

Ya ce: “Wannan dandanzon mata da matasa da ka gani sun fito ne domin yin kira ga Sanata Halliru Dauda Jika da ya fice daga jam’iyyar APC ya shiga jam’iyyar NNPP domin ya samu damar yin takarar gwamnan Jihar Bauchi a 2023.”

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

“Daman mun gargadi uwar jam’iyyar APC ta dauki tikitin neman takarar gwamna ta bai wa Sanata Jika saboda shi ne yake tare da mutane, shi ne yake mutunta mutane, shine ya san matsalolinsu, shine yake kawo cigaba ga kuma shine suke so, sabanin wanda aka zo aka kakaba mana da karfin tsiya. Don haka muke son ya bar jam’iyyar ya koma NNPP mu kuma muna tare da shi dari bisa dari.

“Don haka mu a matsayinmu na mata da matasa muna nuna wa Sanata Jika hanyar da ya dace na cewa ya zo ya bi abun da jama’a ke so. Abun da jama’a ke so kuma shine ya shiga NNPP ya mana takarar gwamna.”

Mata

Abdullahi Kobi ya bada tabbacin cewa muddin Jika ya amince ya fito neman takarar gwamna a NNPP tabbas jama’an jihar za su zabeshi domin sun amince da salon jagorancinsa da kyautata musu, “al’umma ke kawo mutum musamman mata. Ka ga kuwa al’ummar ne suka ce lallai ya zo ya musu takara. Don haka muna da kyakkyawar fatan shine zai yi nasara a babban zaben 2023.”

A bangarenta, Malama Saliha Abubakar ta bayyana cewar a shirye suke su shiga lungu da sako domin nema wa Sanata Jika kuri’u, tana mai cewa sun amince da cewa ya fi kowani dan takara dacewar da zai iya jagorantar jihar Bauchi yadda ya kamata.

“Mu iyaye mata mune mu kan irin halin da muke cikin a hali yanzu. Don haka muna rokon ya amsa kiran mu ya koma NNPP domin mu mara masa baya.”

Da ya ke amsar bukatun kungiyoyin a madadin Sanatan, Haruna Muhammad daya daga cikin hadiman Sanata Jika, ya gode wa kungiyoyin bisa nuna damuwa da soyayya ga Sanata Halliru Dauda Jika ya kuma ba su tabbacin cewa za su yi zama na musamman kan wannan bukatar tare da daukan matakin da ya dace domin cigaban jihar Bauchi.

Ya ce, tabbas Sanata Jika na yi ne don al’umma kuma zai sauraro bukatunsu tare da yin abun da dace. Ya ba su tabbacin cewa da izinin Allah Sanata Jika zai yi takarar gwamna a 2023.

Mata
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Next Post
Ku Ci Gaba Da Yada Labaran Cin Zarafin Mata Da Kananan Yara —CITAD

Ku Ci Gaba Da Yada Labaran Cin Zarafin Mata Da Kananan Yara —CITAD

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.