• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kuri’un ‘Yan Nijeriya Ne Za Su Yanke Hukuncin Lashe Zabe – INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta tabbatar da cewa kuri’un ‘yan Nijeriya ne kadai zai tabbar da wanda ya yi nasarar lashe zabe a 2023.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu shi ya tabbatar da hakan lokacin da yake tarbar tawagar wakilan Majalisar Dinkin Duniya a Abuja.

Ya kara da cewa hukumar zabe za ta yi duk abin da ya dace wajen ganin babban zabe a Nijeriya ya ci gaba da karbuwa a idon duniya.

Ya ce, “Nina mai tabbatar muku cewa za mu ci gaba da duk abubuwan da suka dace da doka wajen ganin ‘yan Nijeriya sun zabi shugabanninsu ta hanyar da ya kamata.

“Kuri’un ’yan Nijeriya ne kadai zai tabbatar da wanda ya samu nasarar lashe zabe a 2023, sannan kuma za mu ci gaba da mutunta zaben ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

“Ina mai tabbatar muku cewa ba za mu taba rintsawa ba har sai mun tabbatar an gudanar da sahihin zabe a Nijeriya ta yadda dimokuradiyya za ta zauna da kafarta. Mun ji dadin kasancewa da ku kuma muna sa ran za su gan ku lokacin gudanar da babban zabe a 2023,” in ji shi.

Farfesa Yakubu ya ci gaba da cewa hukumarsa za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da jam’iyyun siyasa da kungiyoyin fararen huda da ‘yan jarida da jami’an tsaro da kawayenta na kasa da kasa kamar irin su UNOWAS.

“A duk lokacin da muka zo kan wannan manufar, muna samu gwarin gwiwa wajen ci gaba da gudanar da abubuwa yadda ya dace, akwai abun da muke bukata shi ne zaman lafiya da lumana a yankunamu.”

Farfaesa Yakubu ya gode wa UNOWAS bisa a ko da yaushe take turo tawaga wadanda za su saka ido a lokacin gudanar da zabe a Nijeriya.

Da yake gabatar da jawabi, wakili na musamman ga Sakataren Majalisan Dinkin Duniya kuma shugaban UNOWAS a yankin Yammacin Afirka, Mahamat Saleh, ya bayyana cewa zaman lafiya da lumana a Nijeriya shi ne babban burinsu.

Ya ce, “Mun zo Nijeriya ne a wannan lokaci bisa shirye-shiryen babban zabe a 2023. A wurinmu zaman lafiya da lumana da tsaro a Nijeriya shi ne babban burinmu. A ko da yaushe ina matukar yin misali da Nijeriya, muna murna ganin yadda aka zabi ‘yan takara.

“Majalisar Dinkin Duniya za ta ci gaba da goyon bayan Nijeriya domin ganin an gudanar da zabe cikin zaman lafiya da lumana. Muna taya ka murna kuma za mu goyi bayanka kan ayyukan da ka gudanarwa da wadanda kake kokarin yi a wannan zabe mai zuwa,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Murabus Din Babban Jojin Nijeriya Ibrahim Tanko

Next Post

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

2 days ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 days ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

1 week ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

1 week ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 weeks ago
Next Post
2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba  — Ango Abdullahi

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.