• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kuri’un ‘Yan Nijeriya Ne Za Su Yanke Hukuncin Lashe Zabe – INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta tabbatar da cewa kuri’un ‘yan Nijeriya ne kadai zai tabbar da wanda ya yi nasarar lashe zabe a 2023.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu shi ya tabbatar da hakan lokacin da yake tarbar tawagar wakilan Majalisar Dinkin Duniya a Abuja.

Ya kara da cewa hukumar zabe za ta yi duk abin da ya dace wajen ganin babban zabe a Nijeriya ya ci gaba da karbuwa a idon duniya.

Ya ce, “Nina mai tabbatar muku cewa za mu ci gaba da duk abubuwan da suka dace da doka wajen ganin ‘yan Nijeriya sun zabi shugabanninsu ta hanyar da ya kamata.

“Kuri’un ’yan Nijeriya ne kadai zai tabbatar da wanda ya samu nasarar lashe zabe a 2023, sannan kuma za mu ci gaba da mutunta zaben ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

“Ina mai tabbatar muku cewa ba za mu taba rintsawa ba har sai mun tabbatar an gudanar da sahihin zabe a Nijeriya ta yadda dimokuradiyya za ta zauna da kafarta. Mun ji dadin kasancewa da ku kuma muna sa ran za su gan ku lokacin gudanar da babban zabe a 2023,” in ji shi.

Farfesa Yakubu ya ci gaba da cewa hukumarsa za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da jam’iyyun siyasa da kungiyoyin fararen huda da ‘yan jarida da jami’an tsaro da kawayenta na kasa da kasa kamar irin su UNOWAS.

“A duk lokacin da muka zo kan wannan manufar, muna samu gwarin gwiwa wajen ci gaba da gudanar da abubuwa yadda ya dace, akwai abun da muke bukata shi ne zaman lafiya da lumana a yankunamu.”

Farfaesa Yakubu ya gode wa UNOWAS bisa a ko da yaushe take turo tawaga wadanda za su saka ido a lokacin gudanar da zabe a Nijeriya.

Da yake gabatar da jawabi, wakili na musamman ga Sakataren Majalisan Dinkin Duniya kuma shugaban UNOWAS a yankin Yammacin Afirka, Mahamat Saleh, ya bayyana cewa zaman lafiya da lumana a Nijeriya shi ne babban burinsu.

Ya ce, “Mun zo Nijeriya ne a wannan lokaci bisa shirye-shiryen babban zabe a 2023. A wurinmu zaman lafiya da lumana da tsaro a Nijeriya shi ne babban burinmu. A ko da yaushe ina matukar yin misali da Nijeriya, muna murna ganin yadda aka zabi ‘yan takara.

“Majalisar Dinkin Duniya za ta ci gaba da goyon bayan Nijeriya domin ganin an gudanar da zabe cikin zaman lafiya da lumana. Muna taya ka murna kuma za mu goyi bayanka kan ayyukan da ka gudanarwa da wadanda kake kokarin yi a wannan zabe mai zuwa,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Murabus Din Babban Jojin Nijeriya Ibrahim Tanko

Next Post

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

7 hours ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

8 hours ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

1 week ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

2 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

3 weeks ago
Next Post
2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba  — Ango Abdullahi

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

LABARAI MASU NASABA

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

June 14, 2025
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi

June 14, 2025
Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

June 14, 2025
Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

June 14, 2025
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

June 14, 2025
Tinubu

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

June 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

June 14, 2025
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

June 14, 2025
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

June 14, 2025
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.