• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kuri’un ‘Yan Nijeriya Ne Za Su Yanke Hukuncin Lashe Zabe – INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta tabbatar da cewa kuri’un ‘yan Nijeriya ne kadai zai tabbar da wanda ya yi nasarar lashe zabe a 2023.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu shi ya tabbatar da hakan lokacin da yake tarbar tawagar wakilan Majalisar Dinkin Duniya a Abuja.

Ya kara da cewa hukumar zabe za ta yi duk abin da ya dace wajen ganin babban zabe a Nijeriya ya ci gaba da karbuwa a idon duniya.

Ya ce, “Nina mai tabbatar muku cewa za mu ci gaba da duk abubuwan da suka dace da doka wajen ganin ‘yan Nijeriya sun zabi shugabanninsu ta hanyar da ya kamata.

“Kuri’un ’yan Nijeriya ne kadai zai tabbatar da wanda ya samu nasarar lashe zabe a 2023, sannan kuma za mu ci gaba da mutunta zaben ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

“Ina mai tabbatar muku cewa ba za mu taba rintsawa ba har sai mun tabbatar an gudanar da sahihin zabe a Nijeriya ta yadda dimokuradiyya za ta zauna da kafarta. Mun ji dadin kasancewa da ku kuma muna sa ran za su gan ku lokacin gudanar da babban zabe a 2023,” in ji shi.

Farfesa Yakubu ya ci gaba da cewa hukumarsa za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da jam’iyyun siyasa da kungiyoyin fararen huda da ‘yan jarida da jami’an tsaro da kawayenta na kasa da kasa kamar irin su UNOWAS.

“A duk lokacin da muka zo kan wannan manufar, muna samu gwarin gwiwa wajen ci gaba da gudanar da abubuwa yadda ya dace, akwai abun da muke bukata shi ne zaman lafiya da lumana a yankunamu.”

Farfaesa Yakubu ya gode wa UNOWAS bisa a ko da yaushe take turo tawaga wadanda za su saka ido a lokacin gudanar da zabe a Nijeriya.

Da yake gabatar da jawabi, wakili na musamman ga Sakataren Majalisan Dinkin Duniya kuma shugaban UNOWAS a yankin Yammacin Afirka, Mahamat Saleh, ya bayyana cewa zaman lafiya da lumana a Nijeriya shi ne babban burinsu.

Ya ce, “Mun zo Nijeriya ne a wannan lokaci bisa shirye-shiryen babban zabe a 2023. A wurinmu zaman lafiya da lumana da tsaro a Nijeriya shi ne babban burinmu. A ko da yaushe ina matukar yin misali da Nijeriya, muna murna ganin yadda aka zabi ‘yan takara.

“Majalisar Dinkin Duniya za ta ci gaba da goyon bayan Nijeriya domin ganin an gudanar da zabe cikin zaman lafiya da lumana. Muna taya ka murna kuma za mu goyi bayanka kan ayyukan da ka gudanarwa da wadanda kake kokarin yi a wannan zabe mai zuwa,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba  — Ango Abdullahi

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.