ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kuri’un ‘Yan Nijeriya Ne Za Su Yanke Hukuncin Lashe Zabe – INEC

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta tabbatar da cewa kuri’un ‘yan Nijeriya ne kadai zai tabbar da wanda ya yi nasarar lashe zabe a 2023.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu shi ya tabbatar da hakan lokacin da yake tarbar tawagar wakilan Majalisar Dinkin Duniya a Abuja.

Ya kara da cewa hukumar zabe za ta yi duk abin da ya dace wajen ganin babban zabe a Nijeriya ya ci gaba da karbuwa a idon duniya.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Nina mai tabbatar muku cewa za mu ci gaba da duk abubuwan da suka dace da doka wajen ganin ‘yan Nijeriya sun zabi shugabanninsu ta hanyar da ya kamata.

“Kuri’un ’yan Nijeriya ne kadai zai tabbatar da wanda ya samu nasarar lashe zabe a 2023, sannan kuma za mu ci gaba da mutunta zaben ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Ina mai tabbatar muku cewa ba za mu taba rintsawa ba har sai mun tabbatar an gudanar da sahihin zabe a Nijeriya ta yadda dimokuradiyya za ta zauna da kafarta. Mun ji dadin kasancewa da ku kuma muna sa ran za su gan ku lokacin gudanar da babban zabe a 2023,” in ji shi.

Farfesa Yakubu ya ci gaba da cewa hukumarsa za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da jam’iyyun siyasa da kungiyoyin fararen huda da ‘yan jarida da jami’an tsaro da kawayenta na kasa da kasa kamar irin su UNOWAS.

“A duk lokacin da muka zo kan wannan manufar, muna samu gwarin gwiwa wajen ci gaba da gudanar da abubuwa yadda ya dace, akwai abun da muke bukata shi ne zaman lafiya da lumana a yankunamu.”

Farfaesa Yakubu ya gode wa UNOWAS bisa a ko da yaushe take turo tawaga wadanda za su saka ido a lokacin gudanar da zabe a Nijeriya.

Da yake gabatar da jawabi, wakili na musamman ga Sakataren Majalisan Dinkin Duniya kuma shugaban UNOWAS a yankin Yammacin Afirka, Mahamat Saleh, ya bayyana cewa zaman lafiya da lumana a Nijeriya shi ne babban burinsu.

Ya ce, “Mun zo Nijeriya ne a wannan lokaci bisa shirye-shiryen babban zabe a 2023. A wurinmu zaman lafiya da lumana da tsaro a Nijeriya shi ne babban burinmu. A ko da yaushe ina matukar yin misali da Nijeriya, muna murna ganin yadda aka zabi ‘yan takara.

“Majalisar Dinkin Duniya za ta ci gaba da goyon bayan Nijeriya domin ganin an gudanar da zabe cikin zaman lafiya da lumana. Muna taya ka murna kuma za mu goyi bayanka kan ayyukan da ka gudanarwa da wadanda kake kokarin yi a wannan zabe mai zuwa,” in ji shi.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba  — Ango Abdullahi

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.