• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

by Sulaiman
3 years ago
Zabe

Yanzu dai kwanaki 9 kacal su ka rage a yi zaɓen shugaban ƙasa. Akwai muhimman batutuwa 10 da ya kamata a sani dangane da wannan zaɓe.

 

Mutum miliyan 93.5 su ka yi rajistar zaɓe. Sai dai ba lallai dukkan su ne za su yi zaɓe ba.

  • Na Bai Wa Bankuna Umarnin Wadata Mutane Da Takardun N200 – Emefiele

Zaɓen Nijeriya ya kai kwatankwacin zaɓen sauran ƙasashen Afrika ta Yamma baki ɗaya yawa, idan da a ce za su haɗu su yi zaɓe a rana ɗaya.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

INEC ta buga ƙuri’u miliyan 187 don zaɓen shugaban ƙasa. Za a yi amfani da rabin su a lokacin zaɓen 25 ga Fabrairu. Idan ta kama sai an yi zaɓen raba-gardama, wato zagaye na biyu, sai a yi amfani da sauran rabin ƙuri’un kenan.

 

Jam’iyyu 18 ne su ka fitar da ‘yan takarar shugaban ƙasa a zaɓen ranar 25 ga Fabrairu.

 

Idan ta kama a yi zaɓen raba-gardama, wato zagaye na biyu yayin da zaɓen shugaban ƙasa bai fitar da wanda ya yi nasara ba, to INEC za ta shirya zaɓen a cikin kwanaki 21.

 

Idan kuma ba za a yi zaɓen raba-gardama ba, kuma wani ɗan takarar shugaban ƙasa bai kai ƙara kotu ba, to INEC za ta ƙone sauran ƙarin takardun zaɓe miliyan 93.5 da ta buga.

 

Akwai rumfunan zaɓe 176,846 da za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa. Amma yanzu sun koma 176, 606, saboda INEC ta sanar cewa ba za a yi zaɓe a rumfuna 240 cikin jihohi 28 da FCT Abuja ba.

 

9. Adadin ejan-ejan ɗin da Jam’iyyu 18 za su tura wurin zaɓe ya kai 1,642,386. A cikin su 1,574,301 ejan ne a rumfunan zaɓe, wato ‘polling egents’. Sai 68,088 kuma ejan-ejan ne masu sa-ido wurin tattara sakamakon zaɓe, wato ‘collation egents’.

 

Jihohin Taraba da Imo ne ke da mafi yawan rumfunan da ba za a yi zaɓe a cikin su ba. Yayin da Taraba ke da rumfuna 34, Jihar Imo kuwa har 38.

 

INEC ta ce ta rigaya ta bayar da katin shaidar ejan ga wakilan jam’iyyu a wurin zaɓe da wurin tattara sakamakon zaɓe. Saboda haka ba ta yarda mutum biyu su fito su ce jam’iyyya ɗaya su ke wakilta ba. Ejan ɗaya kaɗai INEC ta sani. Wanda ya yi karambani ko gangancin yi wa INEC shisshigi, za a damƙe shi ya fuskanci hukunci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Next Post
Fasto Ya Mutu A Kokarin Yin Azumin Kwana 40

Fasto Ya Mutu A Kokarin Yin Azumin Kwana 40

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.