• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu dai kwanaki 9 kacal su ka rage a yi zaɓen shugaban ƙasa. Akwai muhimman batutuwa 10 da ya kamata a sani dangane da wannan zaɓe.

 

Mutum miliyan 93.5 su ka yi rajistar zaɓe. Sai dai ba lallai dukkan su ne za su yi zaɓe ba.

  • Na Bai Wa Bankuna Umarnin Wadata Mutane Da Takardun N200 – Emefiele

Zaɓen Nijeriya ya kai kwatankwacin zaɓen sauran ƙasashen Afrika ta Yamma baki ɗaya yawa, idan da a ce za su haɗu su yi zaɓe a rana ɗaya.

 

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

INEC ta buga ƙuri’u miliyan 187 don zaɓen shugaban ƙasa. Za a yi amfani da rabin su a lokacin zaɓen 25 ga Fabrairu. Idan ta kama sai an yi zaɓen raba-gardama, wato zagaye na biyu, sai a yi amfani da sauran rabin ƙuri’un kenan.

 

Jam’iyyu 18 ne su ka fitar da ‘yan takarar shugaban ƙasa a zaɓen ranar 25 ga Fabrairu.

 

Idan ta kama a yi zaɓen raba-gardama, wato zagaye na biyu yayin da zaɓen shugaban ƙasa bai fitar da wanda ya yi nasara ba, to INEC za ta shirya zaɓen a cikin kwanaki 21.

 

Idan kuma ba za a yi zaɓen raba-gardama ba, kuma wani ɗan takarar shugaban ƙasa bai kai ƙara kotu ba, to INEC za ta ƙone sauran ƙarin takardun zaɓe miliyan 93.5 da ta buga.

 

Akwai rumfunan zaɓe 176,846 da za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa. Amma yanzu sun koma 176, 606, saboda INEC ta sanar cewa ba za a yi zaɓe a rumfuna 240 cikin jihohi 28 da FCT Abuja ba.

 

9. Adadin ejan-ejan ɗin da Jam’iyyu 18 za su tura wurin zaɓe ya kai 1,642,386. A cikin su 1,574,301 ejan ne a rumfunan zaɓe, wato ‘polling egents’. Sai 68,088 kuma ejan-ejan ne masu sa-ido wurin tattara sakamakon zaɓe, wato ‘collation egents’.

 

Jihohin Taraba da Imo ne ke da mafi yawan rumfunan da ba za a yi zaɓe a cikin su ba. Yayin da Taraba ke da rumfuna 34, Jihar Imo kuwa har 38.

 

INEC ta ce ta rigaya ta bayar da katin shaidar ejan ga wakilan jam’iyyu a wurin zaɓe da wurin tattara sakamakon zaɓe. Saboda haka ba ta yarda mutum biyu su fito su ce jam’iyyya ɗaya su ke wakilta ba. Ejan ɗaya kaɗai INEC ta sani. Wanda ya yi karambani ko gangancin yi wa INEC shisshigi, za a damƙe shi ya fuskanci hukunci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Likitoci Sinawa Ke Tallafawa Masu Larurar Ido A Ghana

Next Post

Fasto Ya Mutu A Kokarin Yin Azumin Kwana 40

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

3 days ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

4 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

5 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

6 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 week ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
Fasto Ya Mutu A Kokarin Yin Azumin Kwana 40

Fasto Ya Mutu A Kokarin Yin Azumin Kwana 40

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.