• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mun Cire Sunayen Mutanen Da Suka Yi Rajistar Katin Zabe Sau Biyu —INEC

by Sulaiman
3 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta bayyana cewa ta yi fatali da sunayen waɗanda su ka yi rajistar zaɓe sau biyu masu yawa.

A nan, hukumar na magana ne kan waɗanda su ka yi rajista daga 15 ga Janairu zuwa 31 ga Yuli, 2022.

  • INEC Ta Dakile Yunkurin Kutse Cikin Rumbun Adana Bayananta – Farfesa Yakubu

Kakakin Yaɗa Labaran hukumar, Festus Okoye ne ya bayyana haka a ranar Litinin, cikin wata sanarwar da ya raba wa kafafen yaɗa labarai.

Ya ce an tsame sunayen ta hanyar amfani da na’urar tantance rajistar sunayen da aka shigar fiye da sau ɗaya (ABIS).

Ya ce akwai ƙa’idojin da INEC ta shimfiɗa, waɗanda idan wanda ya yi rajista bai cika su daidai ba, to za a cire sunansa ne kawai.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Okoye ya ce an kammala aikin tsame sunayen, kuma nan ba da daɗewa ba za a bayyana waɗanda su ka yi rajista daidai, yayin da za a haɗa sunayen na su da sunayen waɗanda aka yi wa rajista a baya.

Daga nan ya ce za a fara rabon Katin Shaidar Rajista (PVC) a ƙarshen Oktoba da kuma farkon Nuwamba.

Idan za a iya tunawa, INEC ta ce waɗanda su ka yi rajista tsakanin Yuni 2021 zuwa Janairu 2022, su 2,523,458 ne, amma da ka tankaɗe waɗanda waɗanda ba su yi rajista daidai ba, an tsame sunaye 1,126,359.

A farkon Disamba ne dai INEC ta ce ta fara tsame sunayen waɗanda su ka yi rajista sau biyu ko fiye da haka.

A cikin labarin, an ruwaito Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta bayyana fara aikin tsame sunayen waɗanda su ka yi rajistar mallakar katin zaɓe sau biyu ko fiye da haka.

Shugaban INEC Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka, lokacin da ya ke jawabi a wurin taron masu ruwa da tsaki, kan bitar fayyace ƙa’idojin zaɓe a sansanin masu gudun hijira.

An shirya taron ne ranar Talata a Abuja, inda Yakubu ya ce sake nazarin tsare-tsaren ya zama wajibi, domin rabon da a sake bibiyar sa tun na ƙarshe da aka yi a 2018, kafin zaɓen 2019.

Ya ce ana nan ana ci gaba da tsame sunayen da aka yi rajista sau biyu ko fiye da haka ana zubarwa, domin a tabbatar da cikakkun adadin yawan waɗanda za su mallaki katin rajistar zaɓe guda ɗaya tilo, kamar yadda doka ta tanadar.

Ya ce sai an kammala tsame sunayen masu rajistar fiye da sau ɗaya sannan za a bayyana ranar da za a liƙa sunayen masu rajista, kowa ya gani a faɗin ƙasar nan.

“A tsarin ganin an gudanar da zaɓuka cikin sansanin ‘yan gudun hijira, mu na so mu tabbatar cewa wannan tsari kamar yadda doka ta tanadar, ba a bar kowa a baya ba.

“Za mu tabbatar kamar yadda dokar zaɓe ta shimfiɗa cewa an gudanar da zaɓe a sansanin masu gudun hijira, kuma naƙasassu sun samu damar yin zaɓe da kuma waɗanda wani Ibtila’i na barin gidajen su ya shafe su, kamar ambaliya.”

Yakubu ya ce aƙalla akwai mutane miliyan uku a sansanonin gudun hijira daban-daban a ƙasar nan.

Ya ce taron sake nazarin su ya zama wajibi a yanzu, saboda masu gudun hijira ɗin sun ƙaru, sakamakon wasu dalilai, kamar ambaliya.

Ya ce a yanzu kuma za a bayar da himma wajen ganin an wayar da kan mazauna sansanonin gudun hijira dangane da muhimmancin zaɓe da kuma ƙa’idojin da doka ta shimfiɗa wajen gudanar da zaɓe a cikin masu gudun hijira.

Shugaban INEC ya musanta zargin da Gamayyar Ƙungiyoyin Kare Haƙƙin Jama’a (CSO) su ka yi wa INEC cewa ta karya dokar Sashe na 19(1) na Dokar Zaɓe, sashen da ya fayyace yadda INEC za ta liƙa sunayen waɗanda su ka yi rajista, domin kowa ya gani a ƙasar nan.

“Ba mu karya wata doka ba. Saboda har yanzu ana kan tantancewa da tsame sunayen waɗanda su ka yi rajista sau biyu ko fiye da biyu tukunna. Idan lokacin da za mu liƙa sunayen ya yi, za mu sanar kowa ya sani, kuma ya gani.” Inji Yakubu.

Ya ce za a liƙa sunayen a dukkan mazaɓu 8,809 da ake da su a ƙasar nan a dukkan ƙananan hukumomi 774 a Nijeriya, kamar yadda Sashe na 19(1) na Dokar Zaɓe ta 2022 ya tanadar.

Ya ce za a haɗa sunayen da aka yi rajista a baya-bayan nan tare da adadin miliyan 84 da ake da su a baya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
Majalisar Dokokin Kano Ta Bukaci Ganduje Ya Biya Kano Pillars Bashin Miliyan 109 Da Suke Bi

Majalisar Dokokin Kano Ta Bukaci Ganduje Ya Biya Kano Pillars Bashin Miliyan 109 Da Suke Bi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.