• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta cimma nasara a aikin da ta yi na gwajin na’urar tantance masu katin shaidar rajistar zaɓe a dukkan jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya, Abuja.

 

Mutane da dama sun jinjina wa hukumar dangane da nasarar da ta samu wajen aikin gwajin na’urar, wato BVAS.

  • 2023: Za Mu Yi Amfani Da Na’urar BVAS Wajen Dakile Magudin Zabe – Farfesa Mahmood

Sun bayyana fatan cewa Allah ya sa a samu irin haka idan an zo yin amfani da na’urar a zaɓen 2023.

 

Labarai Masu Nasaba

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Waɗanda su ka layi aka yi masu gwajin sun ce lallai idan har haka na’urar BVAS ta ke, to za a samu gagarimar nasarar yin sahihin zaɓe kuma karɓaɓɓe a ranar 25 ga Fabrairu da kuma 11 ga Maris.

 

Da yawan su kuma sun haƙƙaƙe cewa babu yadda za a yi maguɗi, rinto ƙuri’u ko aringizo a zaɓen 2023.

 

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce wannan aikin gwajin na’urar BVAS zai bai wa hukumar sa damar ganin inganci da nagartar aikin da BVAS ɗin zai yi, idan an zo zaɓen watan Fabrairu da Maris na wannan shekara.

 

A Jihar Katsina, an yi gwajin na’urar tun daga safe har zuwa ƙarfe 1 na rana.

 

Wakilin mu ya ce ya lura akwai jami’an tsaro da malaman zaɓe a inda aka yi gwajin a Ƙaramar Hukumar Katsina. Ya ce dukkan su sun isa da wuri, kamar yadda aka tsara.

 

Sauran wasu wuraren da ya je sun haɗa da Shinkafi A Gezawa, Sabuwar Bakuru, inda ya iske jami’an tsaro danƙam.

 

An tsara fara gwajin ƙarfe 8:30 na safe zuwa ƙarfe 2 na yamma a faɗin ƙasar nan.

 

Jami’an sun isa da wuri, amma ba su fara aikin ba sai ƙarfe 9 na safe.

 

Zuwa ƙarfe 1.25 na yamma, an tantance mutum 170, wasu 12 ba a tantance su ba.

 

Umaru Shehu daga Mazaɓar Shinkafi A ya shaida wa wakilin mu cewa ya yi matuƙar mamakin yadda tsarin tantance masu rajista da na’urar BVAS ke aiki lafiya ƙalau, ƙeƙe-da-ƙeƙe, kuma a cikin sauri.

 

“Saboda kwata-kwata ko minti biyu ban yi ba, na kammala komai,” inji shi.

 

INEC da kuma masu jefa ƙuri’a sun nuna gamsuwar su dangane da yadda aikin gwajin na’urar tantance masu rajistar zaɓe ya gudana a Gundumar FCT, Abuja.

 

Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya ziyarci wasu rumfunan zaɓen da aka yi tantancewar, ya ce hukumar sa ba ta samu rahoton kasawa, cikas ko tasgaro daga ko’ina ba.

 

INEC ta zaɓi wasu mazaɓu ne daga dukkan jihohin ƙasar nan da Abuja domin ta gudanar da aikin gwajin na’urar tantance masu rajistar zaɓe, wato BVAS, domin ƙara wayar wa da masu zaɓe kai dangane da aikin na’urar.

 

Hakan kuma zai ƙara sa jama’a amincewa da BVAS da kuma rungumar tsarin hannu biyu, ta hanyar yin amanna da sahihancin sa.

 

Yayin da ya ke duba yadda aikin gwajin ya riƙa tafiya, Yakubu ya nuna gamsuwar sa sosai da ingancin BVAS, ganin yadda ba a samu wani cikas ba.

 

“Maƙasudin wannan aikin tantancewar gwaji, shi ne domin a tabbatar da ingancin sa.

 

“A rumfunan zaɓe biyu da mu ka ziyarta, har yanzu ba mu samu rahoton wata matsala da aka fuskanta da BVAS ba. Na’urorin su na aiki sosai. Kuma irin wannan rahoton mu ke samu daga dukkan sasan kasar nan inda aka gudanar da gwajin.”

 

Yakubu ya ce duk inda aka gudanar da gwajin, an tanadi wasu na’urorin, waɗanda waɗanda za a ci gaba da aiki da su idan har wanda ake aiki da shi ya samu matsala. Ya ce a lokacin zaɓen na ranakun 25 ga Fabrairu da 11 ga Oktoba, za a wadatar da BVAS wadatattun da za a iya amfani da wani daga cikin su ya samu mishkila.

 

Ya ce, “Kuma ko da wata na’urar ta samu mishkilar, to akwai ƙwararrun da za su gyara a cikin gaggawa.”

 

Shugaban na INEC ya ce, “Daga irin yadda wannan aikin gwaji ya tabbatar, an samu gagarimar nasara, kuma za a samu nasarar a zaɓen 2023, domin a cikin ƙasa da sakan 30 nau’arar BVAS ke tantance mai sahihiyar rajistar yin zaɓe mutum ɗaya.”

 

Ya ce kuma irin wannan rahoton INEC ta riƙa samu daga dukkan wuraren da aka gudanar da aikin gwajin a faɗin ƙasar nan.

 

Mutane da dama da aka tattauna da su, sun nuna gamsuwa da ingancin BVAS. Wani mai suna Nwani da ya ce shi ba a wannan rumfa ya yi rajista ba, ya ce ya je ne domin ya tabbatar da iƙirarin da INEC ta yi cewa BVAS ɗin da aka kai wannan rumfar zaɓe, ba zai tantance wanda ya yi rajista a wata rumfar zaɓe ba can daban ba.

 

“Ba a nan suna na ya ke ba. Na zo ne ganin-ƙwam. Kuma na bada kati na an duba, sai aka ce min ba a wannan rumfar zaɓen suna na ya ke ba.

 

“Aka saka kati na, amma na’urar BVAS ta ce, ‘a’a, babu sunan ka a wannan rumfar zaɓen.”

 

Yayin da BVAS ya ƙi tantance shi, a gaban sa na’urar ta riƙa tantance waɗanda sunayen su ke a rumfar zaɓen, wato ta Area 10, Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Nijeriya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Da Aka Yi Wa ‘Yan Banga A Katsina

Next Post

2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku

Related

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

49 minutes ago
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

2 hours ago
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu
Labarai

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

2 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe
Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

11 hours ago
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano
Labarai

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

14 hours ago
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

14 hours ago
Next Post
2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku

2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku

LABARAI MASU NASABA

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.