ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mun Yi Nasarar Gwajin Na’urar Tantance Rajistar Zaɓe – INEC

by Sulaiman
3 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta cimma nasara a aikin da ta yi na gwajin na’urar tantance masu katin shaidar rajistar zaɓe a dukkan jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya, Abuja.

 

Mutane da dama sun jinjina wa hukumar dangane da nasarar da ta samu wajen aikin gwajin na’urar, wato BVAS.

ADVERTISEMENT
  • 2023: Za Mu Yi Amfani Da Na’urar BVAS Wajen Dakile Magudin Zabe – Farfesa Mahmood

Sun bayyana fatan cewa Allah ya sa a samu irin haka idan an zo yin amfani da na’urar a zaɓen 2023.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Waɗanda su ka layi aka yi masu gwajin sun ce lallai idan har haka na’urar BVAS ta ke, to za a samu gagarimar nasarar yin sahihin zaɓe kuma karɓaɓɓe a ranar 25 ga Fabrairu da kuma 11 ga Maris.

 

Da yawan su kuma sun haƙƙaƙe cewa babu yadda za a yi maguɗi, rinto ƙuri’u ko aringizo a zaɓen 2023.

 

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce wannan aikin gwajin na’urar BVAS zai bai wa hukumar sa damar ganin inganci da nagartar aikin da BVAS ɗin zai yi, idan an zo zaɓen watan Fabrairu da Maris na wannan shekara.

 

A Jihar Katsina, an yi gwajin na’urar tun daga safe har zuwa ƙarfe 1 na rana.

 

Wakilin mu ya ce ya lura akwai jami’an tsaro da malaman zaɓe a inda aka yi gwajin a Ƙaramar Hukumar Katsina. Ya ce dukkan su sun isa da wuri, kamar yadda aka tsara.

 

Sauran wasu wuraren da ya je sun haɗa da Shinkafi A Gezawa, Sabuwar Bakuru, inda ya iske jami’an tsaro danƙam.

 

An tsara fara gwajin ƙarfe 8:30 na safe zuwa ƙarfe 2 na yamma a faɗin ƙasar nan.

 

Jami’an sun isa da wuri, amma ba su fara aikin ba sai ƙarfe 9 na safe.

 

Zuwa ƙarfe 1.25 na yamma, an tantance mutum 170, wasu 12 ba a tantance su ba.

 

Umaru Shehu daga Mazaɓar Shinkafi A ya shaida wa wakilin mu cewa ya yi matuƙar mamakin yadda tsarin tantance masu rajista da na’urar BVAS ke aiki lafiya ƙalau, ƙeƙe-da-ƙeƙe, kuma a cikin sauri.

 

“Saboda kwata-kwata ko minti biyu ban yi ba, na kammala komai,” inji shi.

 

INEC da kuma masu jefa ƙuri’a sun nuna gamsuwar su dangane da yadda aikin gwajin na’urar tantance masu rajistar zaɓe ya gudana a Gundumar FCT, Abuja.

 

Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya ziyarci wasu rumfunan zaɓen da aka yi tantancewar, ya ce hukumar sa ba ta samu rahoton kasawa, cikas ko tasgaro daga ko’ina ba.

 

INEC ta zaɓi wasu mazaɓu ne daga dukkan jihohin ƙasar nan da Abuja domin ta gudanar da aikin gwajin na’urar tantance masu rajistar zaɓe, wato BVAS, domin ƙara wayar wa da masu zaɓe kai dangane da aikin na’urar.

 

Hakan kuma zai ƙara sa jama’a amincewa da BVAS da kuma rungumar tsarin hannu biyu, ta hanyar yin amanna da sahihancin sa.

 

Yayin da ya ke duba yadda aikin gwajin ya riƙa tafiya, Yakubu ya nuna gamsuwar sa sosai da ingancin BVAS, ganin yadda ba a samu wani cikas ba.

 

“Maƙasudin wannan aikin tantancewar gwaji, shi ne domin a tabbatar da ingancin sa.

 

“A rumfunan zaɓe biyu da mu ka ziyarta, har yanzu ba mu samu rahoton wata matsala da aka fuskanta da BVAS ba. Na’urorin su na aiki sosai. Kuma irin wannan rahoton mu ke samu daga dukkan sasan kasar nan inda aka gudanar da gwajin.”

 

Yakubu ya ce duk inda aka gudanar da gwajin, an tanadi wasu na’urorin, waɗanda waɗanda za a ci gaba da aiki da su idan har wanda ake aiki da shi ya samu matsala. Ya ce a lokacin zaɓen na ranakun 25 ga Fabrairu da 11 ga Oktoba, za a wadatar da BVAS wadatattun da za a iya amfani da wani daga cikin su ya samu mishkila.

 

Ya ce, “Kuma ko da wata na’urar ta samu mishkilar, to akwai ƙwararrun da za su gyara a cikin gaggawa.”

 

Shugaban na INEC ya ce, “Daga irin yadda wannan aikin gwaji ya tabbatar, an samu gagarimar nasara, kuma za a samu nasarar a zaɓen 2023, domin a cikin ƙasa da sakan 30 nau’arar BVAS ke tantance mai sahihiyar rajistar yin zaɓe mutum ɗaya.”

 

Ya ce kuma irin wannan rahoton INEC ta riƙa samu daga dukkan wuraren da aka gudanar da aikin gwajin a faɗin ƙasar nan.

 

Mutane da dama da aka tattauna da su, sun nuna gamsuwa da ingancin BVAS. Wani mai suna Nwani da ya ce shi ba a wannan rumfa ya yi rajista ba, ya ce ya je ne domin ya tabbatar da iƙirarin da INEC ta yi cewa BVAS ɗin da aka kai wannan rumfar zaɓe, ba zai tantance wanda ya yi rajista a wata rumfar zaɓe ba can daban ba.

 

“Ba a nan suna na ya ke ba. Na zo ne ganin-ƙwam. Kuma na bada kati na an duba, sai aka ce min ba a wannan rumfar zaɓen suna na ya ke ba.

 

“Aka saka kati na, amma na’urar BVAS ta ce, ‘a’a, babu sunan ka a wannan rumfar zaɓen.”

 

Yayin da BVAS ya ƙi tantance shi, a gaban sa na’urar ta riƙa tantance waɗanda sunayen su ke a rumfar zaɓen, wato ta Area 10, Abuja.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku

2023: Ibo Mazauna Kano Sun Goyi Bayan Takarar Atiku

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.