• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mutane Miliyan 5 Ne Suka Cancanci Jefa Kuri’a A Kano – REC

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
2023: Mutane Miliyan 5 Ne Suka Cancanci Jefa Kuri’a A Kano – REC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon kwamishinan zabe na Jihar Kano na Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Ambasada Zango Abdu, ya ce INEC ta gama kimtsawa tsaf domin gudanar da sahihi kuma ingataccen zabe a jihar a zaben 2023.

Kan hakan ne kwamishinan, ya ce zuwa yanzu wadanda suka yi rijistar katin zabe kuma suka cancanci kada kuri’a a Jihar Kano sun kai mutum miliyan 5,927,565.

  • Lauyoyin Arewa Sun Zargi EFCC Da Nuna Wariya Kan Wadanda Ake Zargi Da Badakalar Kudade
  • INEC Ta Roki ‘Yan Jarida Da Su Kauce Wa Labarai Da Dumi-Dumi Da Zafafan Kanun Labarai Don Jawo Hankali

Ambasada Abdu, ya bayyana haka ne a lokacin da ke ganawa da masu ruwa da tsaki a dakin taro na ofishin INEC da ke Kano a ranar Juma’a, inda ya ce sun gama shiri wajen gudanar da ayyukansu bisa yadda kundin tsarin mulkin kasa da dokokin zabe suka tanadar.

Abdu ya yi bayanin cewa, dokar zabe sashe na 19 (1) da (2) na dokar zabe ta 2022 ya tanadar da cewa hukumar zabe za ta wallafa kwafin sunayen wadanda suka yi rijistar zabe a kowacr rumfar rijista da ke gudunma da kananan hukumomi.

Bisa wannan dokar, ya ce hukumar ta samar da kwafi na jerin wadanda suka yi rijistar kuma tuni ta manna su a kowace cibiyar rijista guda 484 da ke cikin gundumomi da suke fadin kananan hukumomi 44 na jihar.

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Ya bai wa dukkanin jam’yyun siyasa a jihar tabbacin gudanar da zabe mai cike da gaskiya da adalci.

Ya bukaci masu ruwa da tsakin da su bai wa hukumar hadin kai da goyon baya domin ta samu nasarar cimma wannan manufar ta tabbatar da ingataccen zabe a fadin jihar.

Shi kuma a bangarensa, sabon kwamishinan ‘yansandan Jihar Kano, CP Maman Dauda, ya ce, za su yi aikin hadaka da sauran hukumomin tsaro a jihar don tabbatar zaben ya tafi cikin kwanciyar hankali da tsaro.

Ya yi gargadin cewa duk mai niyyar kawo yamutsi da harigido a lokacin zaben gara ya gaggauta sauya matsayarsa domin ba zai samu gurbin hakan ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: INECJihar LanoKatin ZabeKuri'aRajistaRECZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Sake Zama Mamba A Hukumar Kula Da Harkokin Sufurin Jiragen Sama Ta Kasa Da Kasa 

Next Post

An Gano Halittar Da Ta Fi Girma A Duniya

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

1 hour ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

3 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

5 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

6 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

7 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

12 hours ago
Next Post
An Gano Halittar Da Ta Fi Girma A Duniya

An Gano Halittar Da Ta Fi Girma A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.