• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

by Rabi'at Sidi Bala
4 months ago
2027

An samu radani kan bukatar yi wa ADA rajisata domin zama jam’iyyar siyasa a wurin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC). Ana ganin cewa kungiyar na samun tallafi daga kungiyar hadin gwiwa ta Nijeriya (NNCG).

A cikin wata wasika da aka rubuta a ranar 19 ga Yuni, kungiyar da ke da kudirin zama jam’iyyar ta bayyana cewa ta cika duk wata ka’ida na kundin tsarin mulkin kasar nan da ka’idojin INEC wajen zama jam’iyyar siyasa da ta cancanci yi mata rajista.

  • Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta
  • Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

Sai dai kuma, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya musanta rahotannin da ke cewa shi da sauran shugabannin a cikin NNCG sun amince da ADA ta zama sabon jam’iyyar don kalubalantar Shugaban kasa, Bola Tinubu na jam’iyyar APC a yunkurin sake zabe sa a zaben 2027.

Mashawarcin Atiku kan kafofin yada labarai na zamani, Demola Olarenwaju, ya bayyana cewa har yanzu ana ci gaba da tattaunawa tsakanin shugabannin NNCG, don haka ba a cimma wani matsaya na karshe ba kan yiwuwar amincewa da ADA.

Olarenwaju ya rubuta a shafinsa na Tuwita cewa, “Wani kungiya na kokarin samun rajisata domin zama jam’iyya, kamar kowanne dan Nijeriya, amma tana bukatar yin kawance. Ba a karba kawancen ADA ba, idan lokaci ya yi, za a sanar da jama’a game da batun da kuma matakin da za a dauka. Ku yi hakuri da wannan.”

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A

GORON JUMA’A 8-8-2025

Haka shi ma, shugaban ADC, Cif Ralph Okey Nwosu, ya karyata amincewa da ADA, yana mai cewa batun zama jam’iyya kawance lokaci ya riga ya shude. Ya ce sake bijiro da kawance a hukumance ya faru ne wannan makon, bisa ga shawarar daga dukkan masu ruwa da tsaki.

A cewar wani rahoto, NNCG ta yi rajistar ADA a hukumance ga INEC. Wasikar neman rajistar ADA daga INEC an sanya hannu a kai daga shugaban kungiyar na wucin gadi, Cif Akin A. Rickets, da sakataren kungiyar na wucin gadi, Abdullahi Elayo.

Hadakar ta kuma gabatar da takardu masu muhimmanci, daga cikin su akwai kundin tsarin mulkin jam’iyyar da aka bayar da manufifinra da tambari da kuma bayanan taron kafa ta.

Wasikar ta bayyana cewa alamar masara tana wakiltar juriya da tsafta da muhimman tunani da suke fatan inganta.

“Mun kara hadawa da manufofinmu wacce ta kunshi bayanai game da ra’ayin jam’iyyarmu da kundin tsarin mulkinmu wanda ke bayar da doka da ke bayyana ainihinmu, tsarinmu, da mamufarmu,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

GORON JUMA’A
Goron Juma'a

GORON JUMA’A

August 15, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
GORON JUMA’A 16/05/2025
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 20-06-2025

June 20, 2025
Next Post
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta'adda A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
2027

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.