• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

byYusuf Shuaibu and Sulaiman
3 months ago
ADC

LEADERSHIP ta ruwaito cewa masu neman takarar shugaban kasa a karkashin hadakar jam’iyyar ADC za su sanya hannu a kan yarjejeniyar tallafa wa duk wanda ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.

Wannan yarjejeniya ce da ‘yan takara suka cimma, amma duk da haka, dole ne su gudanar da zaben fid da gwani a tsakaninsu.

  • Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta
  • Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

Tsohon ministan sufuri da kuma babban jigo a hadakar jam’iyyar, Rotimi Amaechi, ya bayyana wa LEADERSHIP hakan yayin wata tattaunawa da shi.

Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar, Sanata Dabid Mark, ya bayyana cewa jam’iyyar ba ta da wanda ta fi so a matsayin dan takara kuma ya tabbatar da cewa a karkashin shugabancinsa, jam’iyyar za ta kai ga nasara.

Mark ya yi wannan bayani ne a daidai lokacin da wasu manyan mambobin hadin gwiwa suke matsa kaimi kan neman tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana burinsa na tsayawa takara a 2027, yayin da yake karban bakuncin tawagar masu ruwa da tsaki daga Gombe a gidansa da ke Abuja a ranar Asabar da ta gabata. Daga bisani, ya musanta cewa ya halarci wani taron da aka matsa masa lamba don ya janye kudirinsa na takara ga yankin kudu.

Haka shi ma, tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, ya bayyana kudirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa, yana mai cewa bai tattaunawa da kowa don ya zama dan takarar mataimakin shugaban kasa a 2027 ba.

Yayin da magoya bayan ‘yan takarar shugaban kasan guda biyu da suka tsaya takara tare a 2019 ke karfafa gwiwar fitowar takarar shugaban kasar Nijeriya, musamman a shafukan sada zumunta, tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi, shi ma ya bayyana aniyarsa ta sake yin takara a zaben shugaban kasa a 2027 karkashin tutar jam’iyyar ADC.

Ya taba takarar shugaban kasa bai samu nasara ba a jam’iyyar APC a 2023, wanda Shugaba Bola Tinubu ya doke shi a zaben fid da gwani. Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bayyana a cikin wata hira cewa ba ya da burin za ma shugaban kasa a halin yanzu.

Amma shi kuwa tsohon dan takarar shugaban kasa na ADC, Dumebi Kachikwu, ya zargi cewa jam’iyyar a karkashin sabuwar jagoranci, tana shirin ba da tikitin ta ga dan arewa, musamman ga Atiku.

Ya yi wannan zargin ne a daidai lokacin da ake zazzafar muhawara kan bayar da takarar shugaban kasa a yankin kudu ko arewa.

Wannan muhawara ta kasance daya daga cikin muhimman abubuwan da suka shafi zaben shugaban kasa na 2023 wanda Shugaban kasa Bola Tinubu na APC ya lashe, wanda ya sanya tikiti ya koma yankin kudanci bayan mulkin shekaru takwas na shugaban kasa Muhammadu Buhari daga arewa.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, Amaechi ya bayyana cewa yarjejeniyar tallafa wa duk wanda ya samu nasarar zama dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar za ta maida hankali ne kan fahimtar juna game da abin da za a kira gudanar sahihin zaben fid da gwani.

Tsohon gwamnan Jihar Ribas ya ce, “Abin da muka yarda a zahiri shi ne, dole ne in ce akwai bukatar a bayyana al’amarin abin da muka yarda shi ne na cewa duk wanda ya zama dan takarar shugaban kasa bisa yadda aka gudanar da sahihin zaben fid da gwani, to dole ne dukkanmu mu mara masa baya.

“Abu na farko shi ne, dole ne mu zauna mu fayyace abin da muke nufi da sahihin zaben fid da gwani, saboda yana da sauki ga wani ya sauya tsarin kuma ya kira shi da suna sahihin zaben fid da gwani,” in ji shi.

Kazalika, sakataren yada labarai na ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya shaida wa LEADERSHIP cewa ba ya san da irin wannan yarjejeniyar ba.

Sakataren yada labaran jam’iyyar ya ce duk da haka jam’iyyar za ta yi iya bakin kokarinta wajen yi wa masu neman takara adalci a dukkan wani mataki.

Bolaji ya ce, “Ba na da masaniya game da wani yarjejeniya a tsakanin ‘yan takara. Abin da jam’iyya ta kudiri niyya shi ne, samar da kyawawan yanayi ga wani dan takara tare da yin adalci a tsananinsu.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version