ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

by Sulaiman and Leadership Hausa
11 months ago
Malam

A yayin cin zarafin malaman makakarantun Boko da wasu iyayen dalibai da wasu ‘yan uwan daliban Nijeriya ke yi, wanda lamarin ke ci gaba zama ruwan dare, kawai saboda malaman, sun hukunta ‘ya’yan kan wani laifi da suka aikata a makarantun su, domin yaran su zamo na gari, amma lamarin, bai isa ga kafafen yada labarai.

Wannan rashin isar cin zarafin na su ga kafafen yada labaran, ya sanya, malaman da irin wannan lamarin ya rutsa da su, ke ci gaba da jurewa, su kuma yi gum, da bakinsu, ba tare da sun gayawa kowa ba.

Irin wannan cin zarfin, ya faru hatta a kan Mista Aledander Rotifa wanda Mataimakin Shugaban Kwalejin Complete Child Debelopment College ne, da ke a yankin Aule, karamar hukumar Akure ta Arewa North jihar Ondo, a ranar 26 ga watan Mayun 2025, inda aka yi zargin wata uwa madam Dorcas Asije, mahaifiya ga wani dalibi sun yi hayar wasu bata gari sun ci zarfin Aledander.

ADVERTISEMENT

Dorcas ta aikata wannan ta’asar kan Aledander ne, don kawai ya kwace wayar salular danta a Kwalejin, a yayin don kar ya aikata magudin jarrabawar WASSCE.

Hakan ya sanya Dorcas tare da wani yayanta wanda tsohon dailibi ne a Kwalejin suka je Kwalejin suka yiwa Aledander barazanar aikakata masa ta’asar na ko dai ya kyale danta ya tabka magun jarrabawar da wayar ta sa, da yake zana darasain lissafi.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Kazalika barazanar ta su bata tsaya nan ba, domin a lokacin da Aledander ke a wani ofishin ‘yansanda, nan ma su bishi har can, tare da bata garin da ta yi haya, inda ta mamayi, wata motar ‘yansandan da ke dauke da Aledander, suka fito da shi waje, suka lakada masa na Jaki.

Sai dai, gwamnatin jihar, ta yi hanzarin shiga lcikin lamarin, inda ‘yansanda, suka cafko Dorcas tare da wasu mutane biyar da ake zargi, suna da hannu, wajen aikata ta’asar.

Kazalika, an gurfanar da su a gaban Kuliya, kan tuhumar hada baki, cin zarfi, barazana ga rayuwarsa, tayar da hayaniya a cikin alumma da kuma yunkurin kisan kai.

Amma mai makon wadanda ake zargin, su nuna damuwa kana abinda ake zargin su, tare da kuma gargadin dan nasu, sai kawai majin Dorcas Mista Elisha Imoukhuede, ya buge da rubata takardar korfi, a kan Aledander da kuma a kan ofishin ‘yansanda na gunduma Okuta Elerinla, zuwa ga Babban Sifetan ‘yansanda.

 

Bugu da kari, a ranar 12 ga watan Okutobar 2021, ‘yansanda sun kama wani uba mai suna Abidemi Oluwaseun mai shekara 35, kan zargin kutsawa cikin Kwalejin mata ta Baptist Girls’ College, da ke a yankin Idi-Aba a garin Abeokuta na jihar Ogun da wasu bata gari, da ya yi hayarsu, suka ci zarafin wani malamin makarantar, saboda kawai, ya zane ‘yarsa, mai shekaru 15 da bulala,

Hakazali, a ranar 16 ga watan Nuwambar 2021, wani dalibain jami’ar Ilorin mai suna Salaudeen Waliyullah Aanuoluwa, ya lakadawa malamar da ke koyarwa a jami’ar, mai suna Madam Zakariyyah duka, inda har ta kai ga, ta suma.

Duka cikin watan na Nuwambar 2021, iyayen wata dalibar makarantar Jericho High School da ke a Ibadan, sun yo hayar wasu bata gari, suka lakadawa wasu malaman makarantar duka

Haka a ranar 13 na watan Fabirairun 2025, mahukutan jami’ar Nnamdi Azikiwe da ke a Awka, a jihar Anambra, sun kori wadi dalibi, mai suna Goddy-Mbakwe Chimamaka Precious, bisa cin zarafin wani malamin jami’ar Dakta Chukwudi Okoye, saboda ya dakatar da ita, daga daukar bidiyo ta hanyar kafar TikTok wanda malamin, ya dakatar da ita.

Kazalika, wani malami a wata makarantar kudi a yankin Abrakaa jihar Delta, a ranar 2 na watan Disambar 2021, ya gamu da ajalisan, bayan da ya sha na Jaki, a hannun wani dalibinsa.

Duba da irin wadannan ayyukan na ta’asar, kan malamai, matsayin mu a wannan Jaridar, muna ganin, ga dukkan alamu, batun duk wata kima da malamai ke da ita, ta fara gushewa, musamman duba da yadda a yanzu, girmama na gaba a tsakanin wasu matasa dalibai, ta kau.

Wani karin babban abin takaicin shi ne, yadda wasu iyaye, ke marawa ‘ya’yansu baya, wajen aikata, manyan laifuka, musaman yadda iyayen ke yin uwa da makarbiya, domin ya’yansu, su aikata magun jarrabawa.

Baya ga wannan, wasu iyayen ma, goyawa ‘ya’yansu baya suke yi, domin rungumar damfarar ta yanar Gizo, da aka fi sani da “yahoo”, domin su zamo masu kudi, a dare daya, wanda kuma an sha ruwaito irin wadannan ‘yan Yahoo, har tsafi da rayukan mutane suna yi, bisa nufin neman sa’a.

Ba wai kawai, an kafa makaranta, domin koyar wa bane, ta kuma kasance, waje ne, na koyar da tarbiyya, amma abin bakin ciki, wasu iyayen dalibai, sun kasance suna yin zagon kasa, maimakon su kara karfafa koyar da da’a a tsakanin ‘ya’yansu daliban.

Ko da yake dai, akwai wasu makarantun, da har yanzu, suke ci gaba da yin kokari wajen dakile cin zarafin da wasu daliban, ke yiwa malamansu.

Muna bayar da shawarar cewa, dole ne, a rinka kare rayuwar malamai yayin da suke kan aikinsu na koyar wa.

Kazalika, muna shawartar ‘yansanda, da su tabatar da an gaggauta daukar mataki, kan lamarin da ya auku na Ondo, musamman domin hakan, ya zama izina ga sauran masu tunanin sake aikata haka.

Malam
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma
  • Sulaiman
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Malam
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam'iyyar PDP Ba — Damagum

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.